An Tura Limami Gidan Kaso bayan Daurawa Masoya Masu Shekaru 16 Aure a Masallaci

An Tura Limami Gidan Kaso bayan Daurawa Masoya Masu Shekaru 16 Aure a Masallaci

  • Kotun Crown da ke Northampton ta yanke wa wani limami hukuncin zama a gidan yari, bayan ya aurar da ’yan shekara 16
  • Limamin, Ashraf Osmani, ya ce bai san an sauya dokar aure a Ingila ba kafin ya jagoranci daurin auren a cikin masallaci
  • Alkalin kotu ya ce babu tilas a auren amma ya soki limamin bisa sakaci, yana mai cewa ya kamata ya san dokar ta sauya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Northampton, England - Wata kotu a kasar Ingila ta yanke wa wani limami hukuncin zaman gidan yari na makonni 15.

Hakan ya biyo bayan samun shi da laifin aurar da yara ’yan shekara 16 a masallaci ba tare da bin ka’ida ba.

An daure liman a masallaci kan jagorantar daura aure
Limami a Ingila, Ashraf Osmani da masallacin da ya jagoranci daurin aure. Hoto: PA Image, Kate Bradbrook/BBC.
Source: Getty Images

Rahoton BBC ya ce Kotun Crown da ke Northampton ta bayyana cewa limamin, Ashraf Osmani mai shekara 52, ya gudanar aure ga matasa biyu a Masallacin Northampton a watan Nuwamban 2023.

Kara karanta wannan

Shehu Sani ya gano dalilin jan kafar sauya shekar Gwamna Abba zuwa APC

Limami ya kare kansa bisa rashin sani

A gaban kotu, Osmani ya bayyana cewa bai san dokar kasar ta sauya ba, wadda ta daga mafi karancin shekarun aure a kasar Ingila zuwa shekara 18, watanni tara kafin faruwar lamarin.

Limamin ya amsa laifinsa a wani zaman kotu da ya gabata, inda aka tuhume shi da laifuka biyu na haddasa auren yara, lamarin da ya sabawa doka.

Alkalin kotun, Mai Shari’a Choudhury, ya ce bincike ya nuna babu wani tilastawa game da aure, kuma matasan sun je wurin limamin ne da kansu ba tare da matsin lamba ba.

Duk da haka, alkalin ya yanke masa hukuncin zaman gidan yari na makonni 15, amma aka dakatar da hukuncin na tsawon shekara guda.

Kotun ta ji cewa matasan sun nemi Osmani ne bayan wani masallaci ya ki aurar da su, inda daga bisani ya amince ya daura musu aure.

Liman ya shiga matsala bayan tura shi gidan kaso
Musulmai suna salla a masallacin a Ingila. Hoto: Aaron Chown/PA Images. (An yi amfani da hoton ne domin misali, ba shi da alaka da labarin).
Source: Getty Images

Ka'idar da limamin ya bi kafin auren

Rahoton kotu ya ce limamin ya karbi kudin fam 50 domin bayar da takardar shaidar aure, sannan bayan bikin, matasan sun yi shagali tare da abokansu, cewar Telegraph.

Kara karanta wannan

Dattawan Katsina sun shiga maganar sakin 'yan bindiga 70, sun zafafa kalamai

Lauyan kare Osmani, James Gray, ya bayyana cewa wannan kuskure daya ne tilo da limamin ya taba yi a cikin shekaru 20 da yake gudanar da nikah.

Ya ce Osmani ya nemi fasfo domin duba ranar haihuwa, ya cike takardun neman aure, kuma ya rubuta bayanan a rajistar masallaci yadda ya dace.

Lauyan ya jaddada cewa duk wadannan matakai na nuna cewa limamin ya aikata kuskuren ne sakamakon rashin sanin sauyin doka, ba da gangan ba.

Sai dai alkalin kotu ya fada masa cewa sakacinsa ne ya jawo matsalar, inda ya ce ya kamata ya san cewa dokar aure ta sauya.

Bayan kammala shari’ar, Ashraf Osmani ya fice daga kotu ba tare da yin wani bayani ba, yana rufe fuskarsa da hannaye da kyalle.

Limami ya rasu yana sallar dare a masallaci

An ji cewa wani Bawan Allah mai suna Sani Lawal ya yi sallama da Duniya a lokacin da yake yin sallar dare domin neman yardar Ubangiji.

Malam Sani Lawal ya rasu ne yayin da yake limancin sallar daren a wani masallaci da ke garin Zaria a jihar Kaduna.

Musulmai su na ta yi wa wannan Alaranman kyakkyawan zato bayan ganin irin karshen da ya yi wanda a Musulunci ake kyautata masa zato.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.