Amurka Ta Yi Barazana, Za a Lafta Haraji a kan Kasashen da ke Mu'amala da Iran

Amurka Ta Yi Barazana, Za a Lafta Haraji a kan Kasashen da ke Mu'amala da Iran

  • Shugaban Amurka, Donald Trump ya yi barazanar kakaba harajin kashi 25 a cikin 100 a kan duk ƙasashen da ke hulɗar kasuwanci da Iran
  • Barazanar haraji ta zo ne a daidai lokacin da Iran ke fuskantar gagarumar zanga-zanga ta adawa da gwamnati, kuma ta zargi Amurka da Isra'ila da hannu a matsalar
  • Tuni kasar China, abokiyar hulda da Iran ta bayyana cewa ba za ta amince da karfa-karfa fa, kuma akwai yiwuwar ta dauki matakin ramuwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

United States of AmericaShugaban Amurka Donald Trump ya yi gargaɗi cewa duk ƙasar da ke yin kasuwanci da Iran za ta fuskanci harajin 25%.

Trump ya bayyana cewa wannan haraji zai fara aiki ne nan take da bare da bata lokaci ba, kuma lamarin ya shafi dukkanin kasashen da ke mu'amala da Iran.

Kara karanta wannan

'Harin sojojin Amurka a Najeriya ya kashe Lakurawa 155,' Rahoto

Amurka ta yi wa abokan huldar Iran barazana
Shugaban Amurka Donald Trump, Jagoran Iran Ayatoullah Khameni Hoto: Getty
Source: Getty Images

Bloomberg ta wallafa cewa Trump ya nanata cewa duk kasar da ke kasuwanci da Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta biya harajin 25% kan duk wata kasuwanci da take yi da Amurka.

Amurka ta dora haraji kan kawayen kasar Iran

Arise News ta ruwaito cewa Shugaban Amurka Donald Trump ya kara da cewa babu gudu ko ja da baya a wannan umarni, sai dai bai yi karin bayani ba.

Rahoton ya ce yawanci kamfanonin Amurka masu shigo da kaya daga ƙasashen waje ne ke biyan irin wannan haraji, amma ba kasashen kai tsaye ba.

Iran, wadda ke cikin ƙungiyar ƙasashen OPEC masu samar da man fetur, ta dade tana fuskantar tsauraran takunkumin Amurka, kuma tana fitar da mafi yawan man feturinta zuwa China.

Trump bai yi karin bayani a kan dalilan barazanarsa ba
Shugaban Amurka, Donald J Trump Hoto: Donald J Trump
Source: Twitter

Sauran manyan abokan kasuwancin kasar Iran sun haɗa da Turkiyya, Iraki, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) da Indiya.

Duk da sanarwar Trump, babu wata takardar hukuma da aka wallafa a shafin White House da ke fayyace tsarin harajin, ko kuma ko harajin zai shafi dukkan ƙasashen da ke hulɗa da Iran.

Kara karanta wannan

Bayan janye korafi a ICPC, Dangote ya kai karar tsohon shugaban NMDPRA a EFCC

Martanin China ga barazanar Amurka

China ta bayyana takaicinta matuka, inda ofishin jakadancinta a Washington ya soki matakin Trump tare da gargaɗin ɗaukar matakan kare muradunta.

Ofishin jakandancin ya ce China za ta ɗauki duk matakan da suka dace kuma ta yi Allah wadai da takunkumin kai-tsaye ba bisa ƙa’ida ba da kuma amfani da danniya.

Barazanar harajin na zuwa ne a lokacin da Iran ke fuskantar mafi girman zanga-zangar adawa da gwamnati cikin shekaru, bayan yaƙin kwanaki 12 da aka yi da Isra’ila a bara.

Trump ya ce Amurka na iya ganawa da jami’an Iran, kuma yana hulɗa da ‘yan adawar kasar, yayin da yake ƙara matsin lamba kan shugabancin Tehran tare da yin barazanar ɗaukar matakin soja.

Iran ta rataye dan leken asirin Amurka

A baya, mun wallafa cewa kasar Iran ta tabbatar da aiwatar da hukuncin kisa kan wani mutum da aka bayyana sunan mutumin a matsayin Ali Ardestani bisa zargin yi wa Isra'ila leken asiri.

Kara karanta wannan

Trump ya yi magana kan Musulmin Najeriya yayin barazanar kawo hare hare

An zargi Ali Ardestani da laifin tattara muhimman bayanai na kasa sannan ya mika su ga hukumar leƙen asirin Isra’ila, wato Mossad, lamarin da Iran ke hukuntawa da hukuncin kisa.

Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da kasar Iran ke ci gaba da fafatawa da Isra’ila a boye, musamman a harkokin leƙen asiri da ayyukan sirri a yankin Gabas ta Tsakiya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng