Abu Ya Girma: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta Baci a Kasashen Yammacin Afirka

Abu Ya Girma: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta Baci a Kasashen Yammacin Afirka

  • Kungiyar ECOWAS ta sanya dokat ta baci a yankin Afirka ta Yamma bayan yunkurin juyin mulkik da sojoji suka yi a jamhuriyar Benin
  • Shugaban hukumar ECOWAS, Omar Touray ya bayyana hakan a taron gaggawa da kungiyar ta kira a birnin tarayya Abuja
  • Ya ce kungiyar ba zata duba ido tana kalllo juyin mulki na kara yaduwa ba, wanda ta ce yana kara jawo barazanar tsaro a yankin

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Kungiyar raya kasashen yammacin Afirka watau ECOWAS ta shiga damuwa tare da fara daukar matakai domin kawo karshen yawaitar junyin mulki a kasashen da ke karkashinta

ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a fadin yankin Afirka ta Yamma a wani bangare na yunkurin dakile barazanar da ke addabar wannan yanki.

Omar Touray.
Shugaban hukumar ECOWAS, Omar Touray. Hoto: @ECOWAS
Source: Twitter

Shugaban hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya sanar da hakan a ranar Talata yayin zaman majalisar sulhu da tsaro ta ministoci karo na 55 da aka yi a Abuja, in ji Tribune Nigeria.

Kara karanta wannan

Juyin mulki: Majalisa ta cimma matsaya kan bukatar Tinubu ta tura sojoji zuwa Benin

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

ECOWAS ta koka kan yawaitar juyin mulki

An kira taron ne saboda yawaitar juyin mulki da yunƙurin juyin mulki da ke faruwa a kasashen yammacin Afirka kwanan nan.

Touray ya ce wadannan abubuwa sun nuna cewa akwai bukatar a yi zurfin tunani kan makomar dimokuraḍiyya da kuma gaggawar zuba jari wajen kare tsaron al’umma.

Ya ce halin da ake ciki a Yammacin Afirka ya kai matakin “babbar barazana”, yana mai cewa daukar wannan matakin ya zama dole domin magance barazanar da juyin mulki ke haifarwa.

Ya jero matslolin da ke tunkarar Afirka ta Yamma ciki har da cikas a tsarin mika mulki ga farar hula a Guinea, raguwa ko takaita damar shiga zaɓe a wasu ƙasashe da kwararar ‘yan ta’adda, masu garkuwa, da ƙungiyoyin ta'addanci.

Omar Touray ya ce zaben yanzu a ƙasashe da dama a yammacin Afirka ya zama abin tayar da rikici maimakon samar da zaman lafiya, kamar yadda Vanguard ta kawo.

Kara karanta wannan

Juyin mulki: Tinubu zai tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin

Mafitar da ECOWAS ta hango

Shugaban hukumar ya yi kira da a riƙa yin taron majalisar sulhu akai-akai kuma a samar da kudi domin yaƙi da ta’addanci, ‘yan fashi da makami da kuma miyagun laifuka a kan iyakoki.

Ya ce lokaci ya yi da ECOWAS za ta dubi makomar dimokuraɗiyya a yankin, domin kiyaye tsarin mulki da zaman lafiya.

ECOWAS.
Taron kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) Hoto: @ECOWAS
Source: Twitter

Alƙawarin ECOWAS ga jama’a

Duk da tsananin ƙalubale, Touray ya tabbatar da cewa kungiyar ba za ta yi biris da al’amuran yankin ba.

"Ba za mu yi shiru ba. Za mu ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da karfafa yankin don amfanin al’ummar mu,” in ji shi.

Juyin mulki: Gwamnoni sun yabi Tinubu

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnonin Najeriya sun ce matakin da Shugaba Bola Tinubu ya dauka na dakile juyin mulki a Jamhuriyar Benin ya ceci Najeriya

Gwamnonin sun ce gaggawar da Tinubu ya yi wajen dakile yunƙurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin ya hana aukuwar babbar barazana ga tsaron Najeriya.

Kara karanta wannan

Barau ya jinjinawa Tinubu da sojojin Najeriya bayan dakile juyin mulki a Benin

Kungiyar NGF ta kuma jinjinawa rundunar sojojin Najeriya bisa gaggawar da suka yi wajen taimakawa wajen tabbatar da zaman lafiya a Benin.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262