'Third World': Najeriya da Kasashe 62 da Trump Zai Hana Mutanensu Zama a Amurka

'Third World': Najeriya da Kasashe 62 da Trump Zai Hana Mutanensu Zama a Amurka

  • Shugaba Donald Trump ya sanar da cewa zai dakatar da mutanen ƙasashen 'Third World' daga samun wurin zama a Amurka
  • Masana sun ce kalmar 'Third World' ta fito ne tun lokacin yakin sunkuru, amma yanzu ana ɗaukarta matsayin kasashe masu tasowa
  • A wannan rahoto, Legit Hausa ta jero kasashen da Trump ya ke nufi da 'Third World' ciki har da Najeriya, Indiya da kuma Iraq

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Amurka - A ranar 28 ga Nuwamba, 2025, Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar cewa zai hana shigowar 'yan hijira daga kasashen 'Third World'.

Wannan mataki da Shugaba Donald Trump ke shirin dauka ya sake tayar da muhawara mai zafi kan ma’anar kalmar da kuma ko ta dace a ci gaba da amfani da ita.

Kara karanta wannan

Ana murnar ceto daliban Maga, 'yan bindiga sun kashe jami'an hukumar NIS a Kebbi

Bayan kalaman Donald Trump, an samu bayanai game da kalmar 'Third World'
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya na jawabi a wani taro da MacDonald ya shirya. Hoto: @WhiteHouse
Source: Twitter

Ma’anar kalmar “Third World” da sauyin da aka samu

Masana tarihi da tattalin arziƙi sun bayyana cewa kalmar Third World ta samo asali ne a lokacin Yakin Baka, kamar yadda aka karanta a wani littafi da aka wallafa a shafin hukumar NIMC.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A wancan lokacin, kalmar na nufin ƙasashen da ba su bi NATO ba ko kuma ƙungiyar Tarayyar Soviet.

Bayan rushewar Tarayyar Soviet a shekarun 1990, ma’anar kalmar Third World ta sauya. Aka dawo amfani da kalmar wajen nuni da:

  • ƙasashen da ke fama da talauci mai tsanani
  • matsalar tattalin arziki da rashin masana’antu
  • karancin albarkatun rayuwa

Sai dai masana sun ce yau kalmar ta zama 'cin fuska', 'marar inganci', kuma bata dace a yi amfani da ita a kasashen duniya a wannan karni ba.

A maimakon haka, cibiyoyi kamar Majalisar Dinkin Duniya da Bankin Duniya suna amfani da kalmomi irin su:

Kara karanta wannan

DSS: Tukur Mamu ya karɓi N50m daga ’yan ta’addan da suka kai hari Kaduna

  • ƙasashen da ke tasowa
  • ƙasashen da suka fi talauci
  • ƙasashen da ke da ƙarancin kudin shiga

Jerin kasashen da ake kira “Third World”

Shugaba Donald Trump ya ce zai duba takardun 'yan kasashe 19 da aka ba izinin zama a Amurka a baya.
Shugaban Amurka Donald Trump ya na rattabu hannu kan wasu takardu a ofishinsa. Hoto: @WhiteHouse
Source: Facebook

A cewar wani rahoto na shafin World Population Review, ga jerin ƙasashen da ake ɗauka a matsayin 'Third World':

  1. Bhutan
  2. Iraq
  3. Eswatini
  4. Tajikistan
  5. Tuvalu
  6. India
  7. Bangladesh
  8. El Salvador
  9. Palestine
  10. Equatorial Guinea
  11. Cape Verde
  12. Namibia
  13. Guatemala
  14. Republic of the Congo
  15. Honduras
  16. Kiribati
  17. São Tomé and Principe
  18. Timor-Leste
  19. Kenya
  20. Ghana
  21. Nepal
  22. Vanuatu
  23. Laos
  24. Angola
  25. Micronesia
  26. Myanmar
  27. Cambodia
  28. Comoros
  29. Zimbabwe
  30. Zambia
  31. Cameroon
  32. Solomon Islands
  33. Uganda
  34. Ivory Coast
  35. Rwanda
  36. Papua New Guinea
  37. Togo
  38. Syria
  39. Mauritania
  40. Najeriya
  41. Tanzania
  42. Haiti
  43. Lesotho
  44. Pakistan
  45. Senegal
  46. Gambia
  47. DR Congo
  48. Malawi
  49. Benin
  50. Guinea-Bissau
  51. Djibouti
  52. Sudan
  53. Liberia
  54. Eritrea
  55. Guinea
  56. Ethiopia
  57. Afghanistan
  58. Mozambique
  59. Madagascar
  60. Yemen
  61. Sierra Leone
  62. Burkina Faso
  63. Burundi.

Kara karanta wannan

Bincike: Ƴan sanda sun bayyana wadanda ake zargi da sace mutane 10 a jihar Kwara

CPC: Trump zai sake tunani kan kasashe 19

A wani rahoton, mun ruwaito cewa, Gwamnatin Donald Trump ta ce za ta sake nazari kan bakin da aka amince masu su zauna a kasar daga kasashe 19.

Hukumar kula da baki a Amurka (USCIS) ta ce ta fara duba damar da aka ba mutanen ƙasashe “masu babbar matsala”, bisa umarnin Trump bayan harbin sojoji.

Har ila yau, Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta dakatar da shigowar baki daga dukkan ƙasashe masu tasowa gaba ɗaya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com