Iran Ta Faɗi Gaskiya kan Illar da Hare Haren Isra'ila Suka Yi Wa Cibiyoyin Nukiliyarta

Iran Ta Faɗi Gaskiya kan Illar da Hare Haren Isra'ila Suka Yi Wa Cibiyoyin Nukiliyarta

  • Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya ce yaki da Isra’ila ya jawo mummunar barna a cibiyoyin nukiliyar kasar
  • Araghchi ya bayyana cewa masana daga Hukumar Makaman Nukiliya ta Iran na binciken hasarar tare da shirya neman diyyar barnar da aka yi
  • Shugaban Amurka Donald Trump ya ce hare-haren da Amurka ta kai sun "lalata" cibiyoyin nukiliya don taimakawa Isra’ila

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Tehran, Iran - Ministan harkokin wajen kasar Iran, Abbas Araghchi, ya yi magana kan barnar da hare-haren Isra'ila suka yi musu.

Araghchi ya fada a ranar Alhamis cewa suna ci gaba da bincike kan barnar da aka yi wa cibiyoyin nukiliya yayin yaƙin da aka yi.

Iran ta yi magana kan yaki da Isra'ila
Iran tana bincike kan barnar da aka yi a cibiyoyin nukiliya. Hoto: Getty Images.
Source: Getty Images

Iran na tattara bayanai kan cibiyoyin nukiliyarta

Rahoton India Today ya ce ministan ya fadi haka ne yayin da kasar ke fara tantance tasirin barnar a Iran a yaƙin kwana 12 da Isra’ila wanda ya kasance “mai tsanani”.

Kara karanta wannan

Trump ya yi tonon silili a taron NATO, ya ce Isra'ila ta sha wuta a hannun Iran

Ya ce masana daga hukumomin makaman nukiliya suna aiki ba dare ba rana domin bincike kan lamarin.

Ya ce:

“Masana daga Hukumar Makaman Nukiliya (na Iran) na gudanar da cikakken bincike kan barnar da aka yi.
“Yanzu, batun neman diyyar wannan barna da bukatar a biya ya shiga cikin manyan batutuwa a ajandar diflomasiyyar kasar.
“Wannan barna mai tsanani ce, kuma binciken masana da yanke shawara a fannin siyasa na gudana a lokaci guda.”
Iran ta yi magana kan barnar da aka yi mata
Iran tana cigaba da bincike domin gano illar hare-haren Isra'ila a kasar. Hoto: Getty Images.
Source: Getty Images

Hari kan nukiliya: Iran ta fasa ganawa da Amurka

Dalilin haka, ministan ya ce Iran ba ta da wani shiri na ganawa da Amurka a makon gobe.

Yayin da yake ganawa da yan jaridu a ranar Alhamis, Araghchi ya karyata ikirarin Shugaba Donald Trump cewa za a yi ganawar mako mai zuwa.

Araghchi ya ce Tehran na ci gaba da tantance ko sake shiga tattaunawa da Washington zai amfani kasar.

Ya ce hakan na da muhimmanci ganin cewa an katse zaman tattaunawa guda biyar da suka gabata sakamakon hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai kan cibiyoyin nukiliya na Iran.

Kara karanta wannan

Iran ta faɗi yawan mutane da ta rasa da masu raunuka bayan yaki da Isra'ila

Abin da Trump ya ce kan nukiliyar Iran

Shugaban Amurka Donald Trump ya sha nanata cewa hare-haren sama da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliya na Iran sun yi barna.

Shugaba Trump ya ce an yi hakan ne domin taimakawa abokiyarta watau kasar Isra’ila saboda lalata wuraren, Vanguard ta ruwaito.

An yi ta samun rahotanni mabanbanta kan harin da Amurka ta kai inda wasu ke cewa babu abin da ya samu cibiyoyin nukiliyar Iran.

Benjamin Netanyahu zai fuskanci tuhuma a Isra'ila

A baya, kun ji cewa kwana 2 da kammala yaƙi da Iran, Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanayahu zai fuskanci shari'a kan zarge-zargen rashawa.

An ce Netanyahu ya roki kotu ta taimaka da ɗage wannan shari'a duba da yanayin da ƙasar ke ciki na yaƙi da kungiyar Hamas da ke Gaza.

Hakan ya biyo bayan maganar Shugaban Amurka, Donald Trump inda ya bukaci a dakatar da wannan shari'a ko kuma a yi wa Netanyahu afuwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.