Trump Ya Yi Tonon Silili a Taron NATO, Ya Ce Isra'ila Ta Sha Wuta a Hannun Iran

Trump Ya Yi Tonon Silili a Taron NATO, Ya Ce Isra'ila Ta Sha Wuta a Hannun Iran

  • Shugaban Amurka Donald Trump ya ce hare-haren da sojojin Amurka suka kai sun rushe cibiyoyin nukiliyar Iran gaba ɗaya
  • Ya bayyana hakan ne a taron shugabannin NATO da ke gudana a Netherlands, inda ya ce tsagaita wuta tsakanin Iran da Isra'ila na tafiya daidai
  • Trump ya ce Iran ta harba manyan makamai da suka yi illa a kasar Isra'ila yayin da suka shafe kwanaki 12 suna gwabza yaki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Netherlands - Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa harin da Amurka ta kai kan cibiyoyin makamashin nukiliya na Iran ya haifar da “cikakken rusau.”

Ya fadi haka ne duk da cewa rahoton sirri ya nuna cewa hare-haren sun jinkirta shirin Iran na ƙirƙirar makaman nukiliya ne na ‘yan watanni kacal.

Kara karanta wannan

Rahoton sirri ya karyata ikirarin Trump na ruguza cibiyar nukiliyar Iran

Trump ya ce an kai hare hare masu zafi zuwa Isra'ila
Trump ya ce an kai hare hare masu zafi zuwa Isra'ila. Hoto: Getty Images
Source: Twitter

TRT ta wallafa cewa Trump ya bayyana haka ne a taron shugabannin ƙasashen NATO da ke gudana a Netherlands.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Donald Trump: An kai hare hare a Isra'ila

Shugaba Donald Trump bayyana cewa makamai masu linzami da Iran ta harba sun ragargaji Isra'ila sosai musamman a kwanakin karshe na yakin.

Baya ga haka, Trump ya bayyana cewa za su iya kulla alaka da Iran a gaba a wani bidiyo da tashar labaran ta wallafa a Facebook.

Trump ya kare matakin Amurka a taron NATO

Trump ya jaddada cewa ba za su taɓa yarda Iran ta ci gaba da haɓaka makamashin nukiliya ba, yana mai cewa an rage wa Iran damar sake kokarin hakan “na tsawon shekaru masu yawa.”

Shugaba Trump ya ce:

“Mun harba makamai masu linzami 30, kuma mun tarwatsa wuraren da Isra’ila ba ta kaiwa hari ba.”

Ya ce wannan mataki ne da ya kawo tsaiko sosai ga burin Iran, kuma hakan ya nuna karfin Amurka da aniyar kare Isra’ila.

Kara karanta wannan

Kwamadan sojojin Iran da ya addabi Isra'ila ya bayyana bayan 'kashe' shi a yaki

Duk da cewa rahoton sirri ya nuna cewa Iran za ta iya dawowa da shirin nata cikin ‘yan watanni, Trump ya yi watsi da rahoton, yana mai cewa:

“Ba zan ce kamar Hiroshima ba ko Nagasaki, amma wannan shi ne abin da ya kawo ƙarshen wancan yakin. Muna son a san cewa wannan hari ne na ƙarshe.”

Barazanar ficewa daga yarjejeniyar nukiliya

Rahotanni daga Tehran sun nuna cewa Iran na tunanin ficewa daga yarjejeniyar hana yaɗuwar makamashin nukiliya (NPT) domin nuna rashin jin daɗi game da hare-haren Isra’ila da Amurka.

Trump dai ya ce yana ganin ana samun ci gaba a yakin Isra’ila da Hamas a Gaza, yana danganta hakan da tasirin harin da Amurka ta kai wa Iran.

Trump ya ce ya gama da Iran kan mallakar nukiliya
Trump ya ce ya gama da Iran kan mallakar nukiliya. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

CNN ta wallafa cewa Trump ya ce:

“Na yi imani da cewa wannan hari da muka kai zai kawo cigaba wajen dakile Hamas. Ya nuna karfinmu,”

Kwamandan Iran ya bayyana bayan 'kashe' shi

A wani rahoton, kun ji cewa shugaban rundunar Amurka, Esmail Qaani ya bayyana a idon duniya bayan kammala yakin Iran da Isra'ila.

Kara karanta wannan

Iran ta fadi mataki na gaba bayan lalata sassan wurin kera makamin nulkiliyarta

Shugaban sojojin ya bayyana ne a wani gangami da 'yan Iran suka shirya bayan tsagaita wuta a yakin da suka yi na kwana 12.

A wani hari da Isra'ila ta kai Iran ne ta bayyana cewa ta kashe Esmail Qaani wanda rashin ganin shi a zahiri ya jawo ce-ce-ku-ce.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng