Donald Trump Ya Tada Hankalin Duniya, Ya Fadi Abin da Zai Faru Idan Bai Ci Zabe Ba

Donald Trump Ya Tada Hankalin Duniya, Ya Fadi Abin da Zai Faru Idan Bai Ci Zabe Ba

  • Tsohon shugaban ƙasan Amurka, Donald Trump ya yi iƙirarin cewa duniya za ta fuskanci yaƙi idan bai lashe zaɓen watan Nuwamba da ke tafe ba
  • Donalɗ Trump ya bayyana cewa ana dab da yaƙin duniya na uku idan bai koma kan mulkin ƙasar Amurka ba
  • Kalaman na Trump na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da faɗa a yankin Gabas ta Tsakiya tsakanin Isra'ila da Hamas

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Amurka - Tsohon shugaban ƙasan Amurka, Donald Trump ya yi iƙirarin cewa za a yi wani babban yaƙi a Gabas ta Tsakiya idan bai ci zaɓen shugaban ƙasa na watan Nuwamba mai zuwa ba.

Donald Trump ya kuma cewa akwai yiwuwar za a yi "yaƙin duniya na uku" idan bai koma kan kujerar mulkin ƙasar Amurka ba.

Kara karanta wannan

Zanga zangar adawa da Tinubu: Minista ya yi magana mai kaushi, ya fadi kulla kullar da ake yi

Donald Trump ya sha alwashi kan zaben Amurka
Donald Trump ya ce za a yi yaki idan bai ci zabe ba Hoto: Win Mcnamee
Asali: Getty Images

Trump ya gana da Netanyahu

Trump ya bayyyana hakan ne bayan ya gana da Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu a gidansa da ke Mar-a-Lago a birnin Florida, ranar Juma'a, cewar rahoton VOA News.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ganawar ta su na zuwa ne kwana ɗaya bayan Netanyahu ya gana a fadar White House da Shugaba Joe Biden da mataimakiyarsa Kamala Harris, rahoton Hindustan Times ya tabbatar.

"Idan muka yi nasara, zai zama da sauƙi. Komai zai yi aiki kuma cikin sauri. Idan ba mu yi ba, za ku ƙare da manyan yaƙe-yaƙe a Gabas ta Tsakiya da wataƙila yakin duniya na uku."
"Kuna kusa da yaƙin duniya na uku fiye da kowane lokaci tun bayan yaƙin duniya na biyu.
"Ba a taɓa samun lokacin da ya yi kusa da hakan ba, saboda muna da mutanen da ba su da ƙwarewa suna mulkar ƙasarmu."

Kara karanta wannan

Rabiu Kwankwaso ya yi magana kan zanga zangar da matasa ke shirin yi a Najeriya

- Donald Trump

Trump ya saba barazanar yin yaƙin duniya

A baya dai tsohon shugaban ya ce duniya na dab da sake ganin ɓarkewar yaƙin duniya saboda faɗan da ake yi a yankin Gabas ta Tsakiya tsakanin Isra'ila da Hamas da kuma mamayar da Rasha ta yiwa Ukraine.

Trump ya kuma yi hasashe mai muni game da abin da ka iya faruwa idan bai yi nasarar sake komawa fadar White House ba, ciki har da iƙirarin cewa kasuwar hannayen jari za ta fadi.

Karanta wasu labaran kan Donald Trump

Bayanai kan wanda ya harbi Donald Trump

A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar binciken manyan laifuka ta FBI ta bayyana sunan Thomas Matthew Crooks a matsayin wanda ya kai hari a yunkurin kashe tsohon shugaban Amurka, Donald Trump.

Matashin da ake zargi da yunƙurin kashe Trump, mai shekaru 20 dan jam'iyyar Republican kamar yadda bayanan zabensa suka nuna. Read more:

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng