Hambararren Shugaban Kasar Gabon Ali Bongo Ya Shaƙi Iskar 'Yanci

Hambararren Shugaban Kasar Gabon Ali Bongo Ya Shaƙi Iskar 'Yanci

  • Sojojin ƙasar Gabon sun saki hamɓararren shugaban ƙasar Ali Bongo bayan shafe kwanaki bakwai a tsare
  • Sun bayyana cewa yana da ikon zuwa duk inda ya ga dama a duniya domin neman maganin rashin lafiyar da ke damunsa
  • Mulkin Ali Bongo dai ya zo ƙarshe ne a ranar Laraba, 30 ga watan Agustan da ya gabata

Libreville, ƙasar Gabon - Sojojin juyin mulkin ƙasar Gabon, sun bayyana sakin hamɓararren shugaban ƙasar Ali Bongo, kwanaki bakwai bayan kifar da gwamnatinsa.

Shugaban mulkin sojin ƙasar, Brice Oligui Nguema ne ya bayyana hakan a cikin wani jawabi na sa da aka watsa a gidan talabijin na ƙasar.

Sojojin dai sun kifar da gwamnatin Bongo ta tsawon shekaru 14, a ranar Laraba, 30 ga watan Agustan da ya gabata kamar yadda Channels TV ta wallafa.

Kara karanta wannan

Minista Ya Bayyana Muhimmin Abu 1 Da Shugaba Tinubu Zai Warware da Zaran Ya Dawo Daga Indiya

Ali Bongo na Gabon ya shaki iskar 'yanci
Sojojin Gabon sun bai wa hamɓararren shugaban kasar Ali Bongo izini fita ƙasar waje. Hoto: @jacksonhinklle
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sojoji sun bai wa hamɓararren shugaban Gabon 'yanci fita ƙasar

Sanarwar ta Nguema ta bayyana cewa Ali Bongo na da 'yancin zuwa duk inda ya ga dama, ciki kuwa har da fita zuwa ƙasashen ƙetare.

Da yake karanto jawaban shugaban mulkin sojin, Kanar Ulrich Manfoumbi Manfoumbi ya ƙara da cewa Ali Bongo ba da damar tafiya ƙasar waje domin neman magana rashin lafiyar da yake fama da ita.

Ali Bongo ya yi fama da matsananciyar shanyewar jiki a watan Oktoban 2018, wanda hakan ya sa ya samu nakasu, ta yadda yake shan wahala wajen motsa kafa da hannunsa ɗaya.

Shugabancin Ali Bongo a Gabon

Hamɓararren shugaban ƙasar Ali Bongo, ya samu damar ɗarewa kan karagar mulkin ne bayan mutuwar mahaifinsa da ya shekara 41 kan mulki wato Omar Bongo, a shekarar 2009.

An sake zaɓar Ali Bongo a karo na biyu a shekarar 2016, sai dai bayan shekaru biyu ne ya gamu da matsalar ciwon shanyewar jiki kamar yadda Africa News ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Hukuncin Kotu: Rabaran Mbaka Ya Gaya Wa Shugaba Tinubu Ya Shirya Barin Ofis? Gaskiya Ta Bayyana

An bayyana Ali Bongo a matsayin wanda ya lashe zaɓen ƙasar na 2023 da aka yi mai cike da rikici, inda aka ce ya samu kaso 64.27%, yayin da abokin hamayyarsa Ondo Ossa, ya samu 30.77%.

Sai dai jim kaɗan bayan ayyana Bongo a matsayin wanda ya lashe zaɓen ne sojojin ƙasar suka sanar da yin juyin mulki.

Ruwanda da Kamaru sun yi wa jami'an tsaronsu garambawul

Legit.ng a baya ta yi rahoto kan sauye-sauyen da kasashen Ruwanda da Kamaru suka yi wa sojojin kasarsu biyo bayan juyin mulkin da aka yi a ƙasar Gabon.

Shugabannin kasashen Afrika da dama sun shiga cikin firgici biyo bayan kwace mulkin Ali Bongo da sojoji suka yi a ƙasar ta Gabon.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng