Abin da Ya Jawowa Jiga-jigan ‘Yan Majalisa Rasa Kujerunsu a Bana – Gbajabiamila

Abin da Ya Jawowa Jiga-jigan ‘Yan Majalisa Rasa Kujerunsu a Bana – Gbajabiamila

  • Femi Gbajabiamila bai ji dadin sakamakon zaben 2023 ba, yana ganin majalisar tarayya tayi rashi
  • Shugaban majalisar wakilan tarayyan kasar ya zargi masu zabe da amfani da addini da kabilanci
  • Gbajabiamila yana ganin ba a duba alheri da cigaban da ‘yan majalisa ke kawowa a mazabunsa ba

Abuja - Femi Gbajabiamila ya koka a kan yadda siyasar shekarar nan ta 2023 tayi aman dadaddun ‘yan majalisar da ake ji da su a mazabun tarayya.

A ranar Laraba, Daily Trust ta rahoto Rt. Hon. Femi Gbajabiamila yana cewa an yi amfani da addini da bangaranci a zaben 25 ga watan Fubrairun 2023.

Shugaban majalisar wakilan tarayyan ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa makonni bayan an shirya zaben.

Gbajabiamila ya ce ba ayi la’akari da irin kokarin ‘yan majalisar a zaben bana ba, abubuwan da suka yi tasiri a guguwar su ne addini da kabilanci.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: Saura kwanaki zabe, an sace dan takarar majalisar dokokin wata jiha

"Wasu ba su yi sa'a ba" - Gbaja

“An sha gumurzu, ba ni kadai ba, har da da yawa daga cikin abokan aikinmu a zauren majalisar nan. Dukkanmu 360, wasu sun yi sa’a, wasu ba su yi ba.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Ina cewa sa’a saboda zaben bai zo yadda ya kamata ba, ba a duba irin kokarin ‘yan majalisar a zauren majalisar tarayya ko kuwa a mazabunsu ba.
Sai dai aka duba wasu abubuwa da-dama dabam. Batun addini ne. Batun kabilanci. Ina sa ran mu cigaba, zabe ya zaba an yi la’akari da kokari.

- Rt. Hon. Femi Gbajabiamila

Gbajabiamila
Rt. Hon. Femi Gbajabiamila da abokan aikinsa Hoto: @SpeakerGbaja
Asali: Facebook

P/Times ta rahoto Hon. Gbajabiamila yana cewa dalilin kawo dokar zabe kenan saboda a kawo gyara a kasa.

‘Dan siyasar yake cewa ya yi bakin kokarinsa na ganin an rika yin amfani da kato da kato wajen tsaida ‘dan takara kafin jam’iyya ta shiga babban zabe.

Kara karanta wannan

Tinubu: "Ban San Batun Kujerar Shugaban Ma’aikatan Fadar Aso Rock ba" - Gbajabiamila

A cewar Gbajabiamila, a zaben tsaida gwani wasu ‘yan majalisar suka rasa damar zarcewa a kujerunsu, da aka shiga babban zabe aka barar da wasu.

Abin da ya faru a zaben nan ba zai taimakawa siyasar Najeriya ba a ra’ayin na uku a kasar.

Nasarar Rufai Hanga

Rahoto ya zo cewa Rufai Hanga ya kafa tarihin zama mutum na farko da ya wakilci Kano ta tsakiya sau biyu a majalisar dattawa, INEC ta ba shi shaida.

Duk da shugaban INEC ya ce ba zai canza Ibrahim Shekarau, a karshe Hanga ya yi nasara a kotu, ya yi abin da tsofaffin gwamnoni biyu ba su iya yi ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel