Hayakin itacen girki na kashe akalla mutum 90,000 kowace shekara a Najeriya, Ministar Yanayi
- Ministar Yanayi ta yi kira ga iyaye mata su rage amfani da itace wajen girki
- A cewarta, hayakin itacen na illa ga su da yaransu kuma har kisa yana yi
- Ministar ta kara da cewa hayakin na da illa ga sararin samaniya
Abuja - Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa hayakin itacen girki na kashe sama da yan Najeriya 90,000, musamman mata da kananan yara a kowace shekara.
Ministar Yanayi, Sharon Ikeazor, ta bayyana hakan a Abuja ranar Talata, a taron kungiyar wayar da kai kan girkin zamani, rahoton DailyTrust.
Ta bayyana cewa:
"Dogaro kan itace wajen girki na daura nauyi kan bishiyoyi a daji."
"Wannan na da hadari kan lafiyar masu amfani da shi, musamman mata dake girki tare da yaransu."
Ta ce shekara bayan shekaru, ma'aikatar yanayi na taimakawa wajen aiwatar da shirye-shiryen samar da hanyoyim girkin zamani domin rage tashin hayakin masu illa ga sararin samaniya."
Asali: Legit.ng
Tags: