Hayakin itacen girki na kashe akalla mutum 90,000 kowace shekara a Najeriya, Ministar Yanayi

Hayakin itacen girki na kashe akalla mutum 90,000 kowace shekara a Najeriya, Ministar Yanayi

  • Ministar Yanayi ta yi kira ga iyaye mata su rage amfani da itace wajen girki
  • A cewarta, hayakin itacen na illa ga su da yaransu kuma har kisa yana yi
  • Ministar ta kara da cewa hayakin na da illa ga sararin samaniya

Abuja - Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa hayakin itacen girki na kashe sama da yan Najeriya 90,000, musamman mata da kananan yara a kowace shekara.

Ministar Yanayi, Sharon Ikeazor, ta bayyana hakan a Abuja ranar Talata, a taron kungiyar wayar da kai kan girkin zamani, rahoton DailyTrust.

Ta bayyana cewa:

"Dogaro kan itace wajen girki na daura nauyi kan bishiyoyi a daji."
"Wannan na da hadari kan lafiyar masu amfani da shi, musamman mata dake girki tare da yaransu."

Kara karanta wannan

Da zafi-zafi: Gwamnatin Neja ta ce za ta sa kafar wando daya da masu ba 'yan bindiga bayanai

Ta ce shekara bayan shekaru, ma'aikatar yanayi na taimakawa wajen aiwatar da shirye-shiryen samar da hanyoyim girkin zamani domin rage tashin hayakin masu illa ga sararin samaniya."

Hayaki itacen girki na kashe akalla mutum 90,000 kowace shekara a Najeriya, Ministar Yanayi
Hayaki itacen girki na kashe akalla mutum 90,000 kowace shekara a Najeriya, Ministar Yanayi
Asali: UGC

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng