Rashin tsaro: IGP Baba ya bayyana yadda ya zama shugaban yan sanda a mawuyacin lokaci

Rashin tsaro: IGP Baba ya bayyana yadda ya zama shugaban yan sanda a mawuyacin lokaci

  • Babban sufeton 'yan sanda na kasa (IGP), Usman Alkali Baba, ya sake jaddada aniyarsa na kawo karshen rashin tsaro a kasar
  • IGP Usman Alkali Baba ya ce Shugaba Muhammadu Buhari ne ya nada shi a mawuyacin lokaci
  • A cewarsa, nan ba da jimawa ba za a dauki sabbin 'yan sanda 20,000 don inganta karfin rundunar

FCT, Abuja - Sufeto Janar na 'yan sanda (IGP), Usman Alkali Baba, ya ce ya karbi ragamar jagorancin rundunar a wani mawuyacin lokaci.

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Baba a lokacin da aka yi tawaye na haramtacciyar Kungiyar ‘Yan asalin yankin Biyafara (IPOB) a watan Afrilu.

Rashin tsaro: IGP Baba ya bayyana yadda ya zama shugaban yan sanda a mawuyacin lokaci
IGP Baba ya bayyana cewa ya zama shugaban yan sanda a mawuyacin lokaci Hoto: Nigeria Police.
Asali: Facebook

Legit.ng ta tattaro cewa tsagerun sun yi kaca -kaca a lokacin inda suka kona ofisoshin 'yan sanda tare da sakin fursunoni.

Kara karanta wannan

Usman Baba Alkali: Na zama IGP a lokacin da a ke tsaka da fuskantar jarabawa

Da yake magana lokacin da ya ziyarci Gwamna Bello Masari na Katsina, Baba ya bayyana wasu kalubalen da rundunar ke fuskanta.

A cewarsa, nan ba da jimawa ba za a dauki sabbin 'yan sanda 20,000 don inganta karfin rundunar.

Yace:

“Na shigo a matsayin IGP a mawuyacin lokaci. Lokacin da na zo, a Kudu maso Gabas da Kudu maso Kudu ne aka yi ta kashe-kashe da suka hada da kashe jami'an tsaro da kuma lalata wuraren aikinmu.
"Yayin da kudu maso kudu da kudu maso gabas ke samun kwanciyar hankali, halin da ake ciki a arewa maso tsakiya da arewa maso yamma na kara yin muni. Za mu dauki ma'aikata daga kowace karamar hukuma a kasar nan. Umurnin shugaban kasa ne cewa ya kamata mu dauki 10,000 don 2020 da kuma wasu 10,000 don 2021."

Kara karanta wannan

Atiku: Ya kamata a kirkiri rundunar 'yan sandan da aikinta shine gadin makarantu

Tun farko a cikin sakonsa, Masari ya ce gwamnatinsa tana kokarin daukar karin ‘yan banga domin karfafa tsaro a jihar.

Gwamnan ya ce 'yan sanda ba su da isassun ma'aikata da kayan aiki don tabbatar da tsaro a jihar, ya kara da cewa za a dauki yan banga a dukkan kananan hukumomi 34 na jihar.

Masari ya ce:

"Daga kiyasin da na yi wa 'yan sanda a kananan hukumomin, ba na tsammanin muna da' yan sanda 3,000 a cikin jihar baki daya."

A wani labari, mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli ya koka kan karuwar harin yan bindiga, yana mai cewa kisar gillar da aka yi wa mace mai juna biyu a Zaria a matsayin abin damuwa.

Daily Trust ta ruwaito cewa sarkin ya ce kasar na cikin wani lokaci mai wahala, yana mai cewa matsalar ba Nigeria kadai ta shafa ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel