An shiga halin fargaba yayin da PDP ta rasa manyan jiga-jiganta 4 cikin makonni 6

An shiga halin fargaba yayin da PDP ta rasa manyan jiga-jiganta 4 cikin makonni 6

  • Jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) reshen jihar Legas tana cikin alhini kan mutuwar manyan jiga-jiganta
  • Adegbola Dominic, shugaban jam'iyyar, ya mutu a ranar Laraba, 25 ga watan Agusta, sakamakon cutar COVID-19
  • Kwanaki kafin rasuwarsa, jam'iyyar ta rasa sakatarenta, Prince Muiz Shodipe-Dosunmu, bayan gajeriyar rashin lafiya

Lagos - Mutuwar shugaban jam'iyyar PDP reshen jihar Legas, Adegbola Dominic, sakataren jam'iyyar, Prince Muiz Shodipe-Dosunmu, da wasu manyan jiga-jigai biyu sun haddasa rikicin shugabanci a tsakanin mambobin.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an samu rudani a cikin jam’iyyar kan wanene sahihin shugaba yayin da ake fafutukar neman kujerar a tsakanin Deji Doherty da Dominic har zuwa rasuwar marigayin.

An shiga halin fargaba yayin da PDP ta rasa manyan jiga-jiganta 4 cikin makonni 6
PDP reshen jihar Lagas ta rasa manyan jiga-jiganta hudu a cikin makonni 6 Hoto: The Cable
Asali: UGC

Jaridar The Punch ta ruwaito cewa shugaban na PDP a jihar Legas ya rasu da yammacin ranar Laraba, 25 ga watan Agusta.

Kara karanta wannan

2023: Kungiyar goyon bayan Osinbajo ta fara kamfen na kasa baki daya, ta ziyarci Gwamna Masari na Katsina

Legit.ng ta tattaro cewa mutuwar Dominic ya kasance kafin na Prince Shodipe-Dosunmu kamar yadda aka ce shugabannin sun mutu ne sakamakon cutar korona.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A cewar rahoton, wani jigon jam'iyyar a Agege, Injiniya Auwal Tahir-Maude, ya ce mambobi da yawa sun shiga rudani game da shugabancin jam'iyyar.

Sauran jiga-jigan jam'iyyar da suka rasu kwanan nan sune; mataimakin shugaban jam’iyyar; Legas ta yamma, Alhaji Monsuru Ajagbe da shugabar mata, Yeye Shola Oladehinbo.

Sakataren yada labarai na PDP na kasa, Kola Ologbondiyan, ya ce bai san da wannan ci gaban ba.

A wani labari na daban, mambobin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a Bamaina da ke karamar hukumar Birnin Kudu ta Jigawa sun bukaci tsohon gwamnan jihar, Sule Lamido da ya tsaya takarar shugaban kasa a 2023.

‘Ya’yan babbar jam’iyyar adawar kasar sun bayyana haka ne a wani karamin taro da aka yi a garin Lamido a ranar Talata, 31 ga watan Agusta, jaridar PM News ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Rikicin PDP ta dawo danya: Uche Secondus ya dira hedkwatar jam'iyyar da dimbin masoya

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng