Wata Ƙungiyar APC Ta Bayyana Wanda Ta Ke So Ya Zama Shugaban Jam’iyyar Na Ƙasa

Wata Ƙungiyar APC Ta Bayyana Wanda Ta Ke So Ya Zama Shugaban Jam’iyyar Na Ƙasa

  • Kungiyar matasan jam'iyyar APC na dandalin sada zumunta a Arewa maso gabas ta goyi bayan Umaru Al-Makura ya zama shugaban jam'iyyar na kasa
  • Kungiyar ta bayyana hakan ne ta bakin mai magana da yawunta, Mu'azu Hina, yayin zantawa da ya yi da manema labarai a garin Gombe
  • Kungiyar ta ce ta gamsu cewa Al-Makura kwararren dan siyasa ne kuma yana da ilimin da zai iya ciyyar da jam'iyyar gaba idan ya zama shugaba

Gombe, Jihar Gombe - Kungiyar Matasan Jam'iyyar All Progressives Congress, dandalin sada zumunta na Arewa maso gabas ta goyi bayan tsohon gwamnan jihar Nasarawa, Umaru Al-Makura a matsayin shugaban APC na kasa, The Punch ta ruwaito.

A cewar rahoton The Punch, mai magana da yawun kungiyar, Mua'azu Hina, ne ya bayyana matsayar jam'iyyar a wani taron manema labarai a Gombe a ranar Asabar, 28 ga watan Agustan 2021.

Kara karanta wannan

Matasan Arewa sun nemi Obansajo ya taimaka a samo mafita ga matsalolin Najeriya

Wata Ƙungiyar APC Ta Bayyana Wanda Ta Ke So Ya Zama Shugaban Jam’iyyar Na Ƙasa
Tsohon gwamnan Nasarawa, Umaru Tanko Al-Makura. Hoto: The Punch
Source: Facebook

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Hina ya ce:

"Bayan tattaunawa da yan jam'iyyar, kungiyoyin mata, matasa da masu ruwa da tsaki a jam'iyyar All Progressives Congress a Arewa maso Gabas da wasu sassan Nigeria, Kungiyar Matasan APC na dandalin sada zumunta a Arewa maso Gabas, ta cimma matsayar cewa Umaru Al-Makura dan siyasa ne da ke kwarewa da ilimi da tabbas zai daukaka jam'iyyar APC.
"Munyi imanin cewa Al-Makura zai saurari kowa kuma zai cika alkawurran da za a yi yayin yakin neman zabe da ke tafe nan gaba a dukkan yankunan kasar."

Wani wakilin Almakura a wurin taron, Dominic Alancha, ya ce tsohon gwamnan ya yi murna da goyon bayan, musamman ganin hakan na zuwa ne daga matasan jam'iyyar wanda sune za su rike jam'iyyar a gaba.

2023: Ba mu buƙatar Atiku ya sake takara, Ya tafi Dubai ya manta da mu tunda ya sha kaye a 2019, Ƙungiyar PDP

Kara karanta wannan

Rikicin Siyasa: Ina Nan Daram a Kan Kujerata, Shugaban PDP Ya Maida Martani

A wani labarin daban, wata kungiya mai suna People’s Democratic Party (PDP) Action 2023, ta bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar kada ya sake takara a shekarar 2023 don ya yi watsi da jam'iyyar ya koma Dubai, UAE, tunda ya fadi zabe a 2019, rahoton Daily Trust.

Atiku, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP a zaben 2019, bai riga ya bayyana niyarsa na son sake takara ba a 2023, amma, dansa, Adamu Atiku Abubakar, ya tabbatar cewa zai sake takara.

Amma a martaninsa, Atikun ya ce ba watsi da jam'iyyar ta PDP ya yi ba, ya tafi yin karatun digiri na biyu ne a kasar waje.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164