Matsalar Tsaro: Babu Sauran Yan Bindiga a Jihata, Gwamnan Arewa

Matsalar Tsaro: Babu Sauran Yan Bindiga a Jihata, Gwamnan Arewa

  • Gwamnan jihar Neja, Abubakar Sani Bello, yace babu sauran yan bindiga a faɗin jihar Neja
  • Gwamnan yace a halin yanzun sai dai yan bindiga su zo daga makotan jihohi su aikata ta'addanci su koma
  • Gwamnan ya kuma jinjina wa jami'an tsaro bisa jajircewarsu tare da alkawarin samar musu da abinda suke bukata

Niger - Gwamna Abubakar Sani Bello na jihar Neja, yace haɗin guiwa tsakanin jihohin da ayyukan yan bindiga ya shafa zai kawo karshen aikata manyan laifukansu na satar mutane.

Gwamnan ya faɗi haka ne yayin da yakai ziyara kauyen Ma'undu, karamar hukumar Mariga, a jihar Neja.

Legit.ng hausa ta gano cewa gaba ɗaya mutanen kauyen sun tsere saboda yawaiyar hare-haren yan bindiga a yankin.

Gwamna Neja, Abubakar Sani Bello
Matsalar Tsaro: Babu Sauran Yan Bindiga a Jihata, Gwamnan Arewa Hoto: Office of the chief press FB Fage
Asali: Facebook

Gwamna Bello ya kai wannan ziyara ne da nufin kara karfafa wa jami'ai 300 da suka haɗa da yan bijilanti a kokarinsu na ceto garin, sanna ya ga irin ɓarnar da aka yiwa mutanen garin.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Matawalle Ya Yi Kira Ga Gwamnatin Buhari Ta Saka Dokar Ta Baci a Arewacin Najeriya

Wannna na kunshe ne a wani rubutu da sakataren yaɗa labarai na gwamnan, Mary Noel-Berje, ya buga a Facebook.

Babu sauran sansanin yan bindiga a Neja

Bello ya bayyana cewa babu sauran yan bindiga a faɗin jihar, inda ya kara cewa suna zuwa ne daga makotan jihohi domin aikata ta'addancinsu.

Gwamna Bello yace:

"Babu sauran sansanin yan bindiga a jihar Neja, yanzun sai dai suzo daga makotan jihohi musamman Zamfara, su aikata ta'addanci su koma. Amma a yanzun babu sauran su a jihar mu."

Zamu cigaba da kokarin tsare al'umma

Bello ya kara da cewa gwamnatinsa zata cigaba da kokarin da take na tsare rayukan al'umma musamman yankunan da lamarin rashin tsaro ya shafa kamar Ma'undu.

Ya kuma jinjina wa jami'an tsaro bisa namijin kokarin da suka yi wajen fatattakar yan bindiga suka bar kauyen tare da alkawarin tallafa musu da kayan aiki da kuma walwala.

Kara karanta wannan

Bayan sama da watanni biyu, daliban Tegina 6 sun mutu hannun yan bindiga

A wani labarin kuma Liyafa Ta Cigaba, Tsohon Shugbaan Kasa Jonathan Ya Samu Babban Mukami a Kasar Waje

An rantsar da tsohon shugaban Najeriya, Dakta Goodluck Jonathan, a matsayin sabon shugaban jami'ar Cavendish, Uganda.

Tsohon shugaban ya zama mutum na uku da zai jagoranci jami'ar tun bayan da aka kafa ta.

Asali: Legit.ng

Online view pixel