Yadda Wasu Fusatattu Mutane Suka Tari Yan Bindiga, Suka Hallaka Daya Daga Ciki a Taraba

Yadda Wasu Fusatattu Mutane Suka Tari Yan Bindiga, Suka Hallaka Daya Daga Ciki a Taraba

  • Wasu mutane sun fusata sun tari yan bindigan da suka kawo musu hari a jihar Taraba
  • Ɓarayin sun kai hari gidan wani hamshakin manomi a ƙauyen Jauro Manu, dake karamar hukumar Gassol
  • Yayin fafatawa da ɓarayin, mutanen gari sun samu nasarar kashe wani ɗan Okada dake tare da ɓarayin

Taraba - Wani ɗan Okada da ake kira da suna Haro ya rasa ransa a ƙauyen Jauro Manu, ƙaramar hukumar Gassol, jihar Taraba, kamar yadda dailytrust ta ruwaito.

Wanda ake zargin dai ya rasa ransa ne yayin da wasu fusatattun mazauna ƙauyen suka ci karfin masu garkuwa da suka kai hari ranar Litinin da dare.

Rahotanni sun bayyana cewa mazauna kauyen sun fito da yawansu lokacin da tawagar masu garkuwa suka kai hari gidan babban manomi, Irimiya Musa.

Kara karanta wannan

Murna Ta Koma Ciki: Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba da Yan Bikin Aure a Jihar Kwara

Wasu mutanen gari sun tari masu garkuwa a Taraba
Yadda Wasu Fusatattu Mutane Suka Tari Yan Bindiga, Suka Hallaka Daya Daga Ciki a Taraba Hoto: punchng.com
Asali: UGC

Wannan ba shine na farko ba

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Wani mazaunin ƙauyen wanda gidansa na daga cikin waɗanda aka kaiwa harin ya shaidawa manema labarai cewa wannan harin shine na uku.

Mutumin yace:

"A harin da suka kawo mana na farko, na samu nasarar tserewa amma sai da suka sace matata da kuma ɗiyata."
"Da farko sun sako ɗiyata inda suka bata layin waya ta bani domin mu tattauna da su game da kuɗin fansa."
"Ɓarayin sun cigaba da rike matata har tsawon kwana uku, amma a kwana na huɗu ta samu tserowa daga hannunsu."

Mutumin ya kara da cewa amma yayin da suka kai masa hari a karo na biyu ba su samu kowa a gidan ba.

Da aka tuntubi kakakin yan sanda na jihar Taraba, ASP Abdullahi Usman, yace yana cikin taro a lokacin.

Kara karanta wannan

Akalla Mutum 5 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Dakarun Sojoji Suka Fatattaki Yan Bindiga a Kaduna

Amma ya yi alkawarin zai sanar a hukumance da zaran ya samu cikakken bayani daga baturen yan sandan yankin.

A wani labarin kuma Abun Farin Ciki Gwamna Zulum Ya Jagoranci Sanya Marayu 5,361 Makaranta a Monguno

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umaru Zulum, ranar Laraba a garin Monguno, ya jagoranci saka marayu 5,361 da rikicin Boko Haram ya kashe iyayensu a makaranta.

Zulum wanda dakansa ya jagoranci ɗaukar bayanan Marayun, ya shafe kwanaki biyu yana gudanar da aikin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262