Cikakken jerin sabbin jihohi 20 da majalisa ke shawarar kirkira a Najeriya

Cikakken jerin sabbin jihohi 20 da majalisa ke shawarar kirkira a Najeriya

  • Majalisar dattawa ta karbi rahoton koke daga yankuna daban-daban na Najeriya kan gyara kudin tsarin mulki
  • A halin yanzu, an ware wasu sassa 20 da ake sa ran su zama sabbin jihohi a Najeriya nan gaba
  • Legit ta kawo muku jerin jihohin da kuma in da za a rabe su su zama jihohi masu zaman kansu

Kwamitin majalisar dattawa kan sake duba kundin tsarin mulkin Najeriya ya ba da shawarar a kirkiro sabbin jihohi 20.

Kwamitin ya cimma wannan matsaya ne bayan ya duba abubuwa daban-daban da suka hada da ikon gwamnatin farar hula na kirkiro jihohi.

Majiyoyi sun shaida wa jaridar The Nation cewa ana iya gudanar da zaben raba gardama a kasa da jihohi 20.

Cikakken jerin sabbin jihohi 20 da majalisa ke shawarar kirkira a Najeriya
Majalisar dattawa | Hoto: @NgrSenate
Asali: Facebook

Kwamitin ya ba da shawarar ba da matsayin jiha ga FCT. An ce jerin bukatun kafa sabbin jahohi sun yi tsawo sosai. Su ne kamar haka:

  1. Jihar ITAI daga Akwa Ibom
  2. Jihar Katagum daga Bauchi
  3. Jihar Okura daga Kogi ta Gabas
  4. Jihar Adada daga Enugu
  5. Jihar Gurara daga Kaduna ta Kudu
  6. Jihar Ijebu daga Ogun
  7. Jihar Ibadan daga Oyo
  8. Jihar Tiga daga Kano
  9. Jihar Ghari daga Kano
  10. Jihar Amana daga Adamawa
  11. Jihar Gongola daga Adamawa
  12. Jihar Mambilla daga Taraba
  13. Jihar Savannah daga Borno
  14. Jihar Okun daga Kogi
  15. Jihar Etiti daga shiyyar kudu maso gabas
  16. Jihar Orashi daga Imo da Anambra
  17. Njaba daga jihar Imo ta yanzu ko rabewar jihar Aba daga Abia
  18. Jihar Anioma daga Delta
  19. Jihohin Torogbene da Oil River, daga jihohin Bayelsa, Delta da Ribas
  20. Jihar Bayajida daga sassan Katsina, Jigawa da Zamfara

Kara karanta wannan

Da duminsa: Tsohon gwamnan jihar Kano lokacin mulkin Abacha ya kwanta dama

Gwamnonin PDP sun magantu bayan ficewar wasu manyan jam'iyyar jiya Talata

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ta yi kira ga mambobi da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da su kwantar da hankulansu kan murabus din wasu mataimaka na jam’iyya bakwai a ranar Talata.

Kungiyar ta yi wannan kiran ne a cikin wata sanarwa da shugabanta kuma gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal ya fitar a Abuja, Daily Nigerian ta ruwaito.

Mista Tambuwal ya bukaci duk mambobin jam'iyyar da abin ya shafa da su yi wa jam'iyyar fatan zaman lafiya, domin kuwa mambobin na ci gaba da kokarin shiga cikin lamarin.

Ya bayyana cewa kungiyar ta yi nadama da bakin ciki na rigingimun da suka faru kwanan nan a PDP.

Sokoto da sauran jihohin Najeriya guda 5, da yadda sunayensu suka samo asali

A wani jerin daban, Najeriya kasa ce da ba wai kawai ta kunshi wadataccen ma'adinai da albarkatun kasa ba, ta kunshi har ma da albarkatu masu ban mamaki. A al'adun Najeriya, babu sunan da ba shi da ma'ana kama daga sunan mutum har zuwa sunan gari.

Kara karanta wannan

Sokoto da sauran jihohin Najeriya guda 5, da yadda sunayensu suka samo asali

Yayin da kowa yasan Najeriya na da jihohi 36 da babban birnin tarayya, ba kowa ne yasan ma'anar sunayen dukkan jihohin ba da kuma yadda suka samo asali.

A cikin wannan rahoton, Legit ta tattaro sunayen wasu jihohi shida da kuma yadda sunayensu suka samu a tarihi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel