Gwamnatin Buhari ta gargadi mazauna waje kan daukar nauyin masu rikita Najeriya

Gwamnatin Buhari ta gargadi mazauna waje kan daukar nauyin masu rikita Najeriya

  • Gwamnatin Najeriya ta gargadi 'yan Najeriya mazauna kasashen waje kan taimakawa tsageru
  • Gwamnatin ta ce, ya kamata mazauna kasashen waje su taimakawa gwamnati don ci gaban kasa
  • Ministan yada labarai da al'adu, Lai Mohammed ne ya bayyana haka yayin wata ganawa da kungiyar NIDO

Lai Mohammed, ministan yada labarai da al'adu, ya gargadi kungiyar 'yan Najeriya mazauna kasashen waje (NIDO) kan daukar nauyin kungiyoyin 'yan aware.

Lai Mohammed ya bayyana haka ne a lokacin da tawagar NIDO, reshen Burtaniya ta kai masa ziyara a ofishinsa ranar Talata, 27 ga watan Yuli.

Ministan ya ce abin takaici ne yadda kungiyoyin 'yan aware da ke fafutuka a duniya kuma suke amfani da wasu mambobin NIDO wajen yada labaran karya game da kasa Najeriya.

Gwamnatin Buhari ta gargadi mazauna kasashen waje kan daukar nauyin masu son rikita Najeriya
Ministan Yada Labarai a Najeriya | dailytrust.com
Asali: UGC

Ya ce wani abin damuwa ma shi ne yadda kungiyoyin 'yan awaren ke dogaro da gudummawar kudade da wasu mambobin NIDO ke bayarwa don gudanar da ayyukansu na barna.

Kara karanta wannan

Minista Lai Mohammed ya magantu kan matsalolin kabilanci da addini a Najeriya

Ministan ya bukace su da su taimaka wa kokarin gwamnati maimakon yada labaran karya da kuma yada “karya" na zarge-zargen cin zarafin addini, wariyar siyasa, da cin zarafin bil adama.

Jaridar Cable ta yanko inda ministan ke cewa:

"Abin takaici ne da kunya yadda wasu 'yan Najeriya mazauna kasashen waje har yanzu suka dogara da dandalin da ke yada labaran bogi da labaran karya game da Najeriya.
“Don haka, ina so in yi amfani da wannan damar in yi kira ga NIDO da ta kwace wannan shiri daga wadanda suka kudiri aniyar bakanta sunan Najeriya a cikin wasu kasashe.
“A matsayin ta na kungiya mai tsari da kuma kyakkyawar alaka, ina rokon NIDO da ta yi hada kai da kungiyoyin gwamnati, kungiyoyin majalisu da cibiyoyin tunani na duniya da ke manyan biranen duniya don taimakawa wajen sauya labarin.
“Ina kuma rokon su da su guji kungiyoyin 'yan aware, masu tayar da kayar baya da masu son tayar da zaune tsaye wadanda ke da niyyar tura labaran karya don su nuna Najeriya na cikin mummunan yanayi.

Kara karanta wannan

An gano yaran makarantar Islamiyyar Tegina a yankin Shiroro

"Ba ni da wata shakka cewa za ku dauki wannan kiran da mahimmanci kuma ku yi duk abinda za ku iya don canza labarin zuwa mafi kyau."

Lai Mohammed ya amince da cewa Najeriya na fuskantar kalubale

Ministan ya ce gwamnati ta amince da kalubalen da kasar ke fuskanta, musamman a bangaren rashin tsaro, kuma tana “kokari” wajen ganin ta magance su.

Ya kara da cewa, gwamnatin tarayya na sake yin wani aiki tare da kara yin kokarin diflomasiyya don dakilewa da kuma juya akalar labarun karya kan Najeriya, baya ga dakile yaduwar farfagandar kin jinin gwamnati.

Lai Mohammed, duk da haka, ya yaba wa mambobin kungiyar NIDO ta Burtaniya saboda kishin kasarsu da kuma “haskaka kasar da kyau”.

Jerin sabbin manyan laifuka 3 da jamhuriyar Benin ke tuhumar Sunday Igboho akai

Ibrahim Salami, daya daga cikin lauyoyin da ke kare Igboho ya bayyana cewa an bijiro da sabbin tuhume-tuhume a kan Sunday Igboho a ranar Litinin, 26 ga watan Yuli, yayin zaman kotu, jaridar The Punch ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Kanu da Igboho: Kungiyar arewa ta dau zafi, ta bayyana abun da ya kamata FG ta yi wa ‘yan bindiga da makiyaya

Wadannan su ne uku daga cikin manyan laifukan da gwamnatin jamhuriyar Benin ke tuhumar Igboho akai:

  1. Hijira ba bisa ka'ida ba
  2. Hadin baki da jami'an shige da fice
  3. Kokarin haifar da tarzoma

PDP ta caccaki tafiyar shugaba Buhari zuwa Landan, ta ce ya yaudari 'yan Najeriya

A wani labarin, Jam'iyyar PDP ta soki tafiyar shugaba Buhari zuwa Landan domin duba lafiya da kuma halartar wani taron koli kan fannin ilimi duk dai a Landan din, jaridar Punch ta ruwaito.

PDP ta ce, tafiyar shugaban ba komai bane face son amfani da albarkatun kasa don halartar taro wanda zai iya halartar ta yanar gizo; kamar yadda wadanda suka shirya taron suka tsara.

PDP ta kuma yi Allah wadai da Fadar Shugaban Kasa kan kokarin boye ganawarsa ta sirri da likitocinsa a karkashin taron da zai halarta, tare da yin tir da rashin cika alkawuran shugaba Buhari na zaben 2015 cewa ba zai je kasar waje domin duba likita ba.

Kara karanta wannan

Bayan Kame Sunday Igboho, Yarbawa sun magantu kan ra'ayin ballewa daga Najeriya

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.

Tags: