Wata mata ta shiga wajen bikin cikarta shekaru 50 a akwatin gawa, bidiyon ya haddasa cece-kuce
- Wata baiwar Allah tayi bikin cikar ta shekaru 50 a cikin wani yanayi da ba a saba gani ba lamarin da ya jefa kafafen sada zumunta cikin rudani
- A cikin bidiyon da ke yawo, matar ta isa wurin da za a yi bikin ranar haihuwar a cikin akwatin gawa na gilashi
- Bayan ta isa cikin yanayi da ba a saba gani ba, an taimaka mata ta fito sannan aka mika mata lasifika inda ta rera waka
Zagayowar ranar haihuwa lokaci ne na musamman a rayuwar mutum kuma wata baiwar Allah ta yi nata cikin wani yanayi da ba za a taba mantawa da shi ba.
Matar wacce ta zama abun magana a shafukan sada zumunta tayi bikin cikar ta shekaru 50 a duniya sannan ta isa wurin taron cikin wani yanayi da ba a saba gani ba.
KU KARANTA KUMA: Kyawawan hotunan ‘yar Najeriya da ta yi wuf da wani Bature, jama’a sun yi cece-kuce

Kara karanta wannan
Kyawawan hotunan ‘yar Najeriya da ta yi wuf da wani Bature, jama’a sun yi cece-kuce

Asali: Instagram
A cikin bidiyon da @gossipboyz1 ya wallafa a Instagram, an kawo matar wurin taron a cikin akwatin gawa na gilashi.
Yayinda ta isa wurin, baƙi sun taimaka mata wajen fitowa daga cikin akwatin. Daga nan sai aka bai wa matar da ba a san ko wacece ba lasifika inda ta rera waka don burge bakin.
An yi cece-kuce kan bidiyon
@goglownatural_skincare ta rubuta:
"Me wannan ke nufi yanzu idan an fada mata cewa za ta mutu yanzu za ta fara kuka.”
@sharon_jamaican_biafan ya ce:
"Menene dalilinta na aikata hakan? Abin rashin tunani da na gani a yau!"
KU KARANTA KUMA: Bidiyo ya nuna lokacin da mai martaba sarkin Kajuru ya fashe da kuka bayan masu satar mutane sun sako shi
@scopicsgg yayi sharhi:
"Ba zan iya kallon zuwa karshen ba, da gaske abubuwa suna faruwa a wannan duniyar."
@pappy_horris ya bayyana:
"Da ta mutu a cikin akwatin ko dai wannan na yiwa Ubangiji ba’a ne.”
A wani labarin, wani mai ikirarin Fasto ne shi mai suna Omosebi Fred, ya gurfana a gaban kotu kan zargin karkatar da kudin cocin har na naira miliyan 15 da rabi.
An gurfanar da Adeola a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke zama a Abuja da Hukumar Yaki da Masu Yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC) kan tuhume-tuhume 11 kan zargin karkatar da kudin cocin.
Zarge-zargen, a cewar hukumar yaki da cin hanci da rashawa, sun hada da zargin "hada baki da cin amanar mukamin ofis da karkatar da kudade."
Asali: Legit.ng