Anga Wata a Najeriya, Sarkin Musulmi Ya Faɗi Ranar da Musulmai Zasu Yi Eld-Eil Kabir 1442AH

Anga Wata a Najeriya, Sarkin Musulmi Ya Faɗi Ranar da Musulmai Zasu Yi Eld-Eil Kabir 1442AH

  • Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar III, ya bayyana ranar Lahadi 11 ga watan Yuli 2021 a matsayin ranar farko a watan Dhul-Hijja
  • Sarkin ya bayyana haka ne biyo bayan samun rahotannin ganin wata a wasu sassan Najeriya da ka yi ranar Asabar
  • Wannan na nufin musulmai a Najeriya zasu gudanar da sallah babba (Eid-el-Fitr) ranar Talata 10 ga Dhul-Hijja

Sarkin Musulumi kuma shugaban majalisar ƙoli ta addinin musulunci a Najeriya, Alhaji Sa'ad Abubakar III, ya bayyana ranar Lahadi 11 ga watan Yuli, 2021 a matsayin 1 ga watan Dhul-Hijja 1442AH, kamar yadda dailytrust ta ruwaito.

KARANTA ANAN: Da Ɗumi-Ɗumi: El-Rufa'i Ya Tabbatar da Mutuwar Tsohon Mataimakin Gwamnan Kaduna

Wannan na ƙunshe ne a wani jawabi da shugaban kwamitin harkokikin addinin musulunci na fadar mai martaba sarkin musulmi dake Sokoto, Farfesa Sambo Junaidu, ya fitar ranar Lahadi.

Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar III
Da Ɗuminsa: Anga Wata a Najeriya, Sarkin Musulmi Ya Faɗi Ranar da Musulmai Zasu Yi Eld-Eil Kabir 1442AH Hoto: dailytrust.com
Asali: UGC

A jawabin nasa, yace:

"Kwamitin dake bada shawarwari kan al'umaran addinin musulunci na fadar sarkin musulmi tare da haɗin guiwar kwamitin duban wata ya samu rahoton ganin jinjirin watan Dhul-Hijja 1442AH."

Kara karanta wannan

Yadda 'yan gudun hijira suka haifi jarirai sama da 17,000 a sansaninsu na jihar Borno

"Mai alfarma sarkin musulmi ya amince da rahoton kuma ya bayyana Lahadi 11 ga watan Yuli a matsayin ranar farko ta watan Dhul-Hijja 1442AH."

"Sarkin musulmi yana taya ɗaukacin al'ummar musulmin Najeriya murna tare da fatana Allah SWT ya cigaba da tsare su da rahamarsa."

An Jawo Hankalin Musulmi su cigaba da addu'an neman zaman lafiya

Alhaji Sa'ad Abubakar ya kuma roƙi al'ummar musulmi da su cigaba da addu'an neman zaman lafiya da cigaban ƙasa yayin da yake taya su murnan sallah babba dake tafe (Eid-el-kabir), kamar yadda premium times ta ruwaito.

Hukumar dillancin labarai a Najeriya NAN, ta ruwaito cewa watan Dhul-Hijja shine wata na 12 daga cikin jerin watannin addinin musulunci.

Watan yana da matuƙar muhimmanci ga musulman duniya, kasancewa a cikinsa ne mabiya addinin musulunci suke aikin hajji ga waɗanda suka samu iko, kuma suke yin layya.

KARANTA ANAN: Bayan Yan Bindiga Sun Sace Sarkin Kajuru, Shugaban Majalisa Ya Yi Zazzafan Martani

Kara karanta wannan

Dr Isa Ali Pantami: Falalar Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijjah

Za'a yi sallah ranar Talata a Najeriya

Saboda bayyana Lahadi 11 ga watan Yuli a matsayin ranar farko a watan Dhul-Hijja 1442AH da sarkin musulmi yayi, al'ummar musulmai zasu gudanar da sallah babba (Eid-el-Kabir) ranar Talata 20 ga watan Yuli.

Ranar tazo dai-dai da 10 ga watan Dhul-Hijja 1442AH, domin a wannan ranar ne ake gudanar da sallah babba.

A wani labarin kuma Illar COVID19: Yadda Magidanta a Najeriya Ke Fama da Hauhawar Farashin Kayan Abinci, Duk da Ƙarancin Kuɗin Shiga

Cutar COVID19 ta yi babbar illa ga yan Najeriya yayin da farashin kayan abinci ya ƙaru kuma kuɗin shiga suka ragu

A samu ɓarkewar cutar a karo na farko ranar 27 ga watan Fabrairu, 2020, kuma ta kashe mutane dama.

Asali: Legit.ng

Online view pixel