Da Ɗuminsa: Gwamna Zulum Ya Shilla Ƙasar Nijar, Ya Sa Labule da Shugaba Bazoum

Da Ɗuminsa: Gwamna Zulum Ya Shilla Ƙasar Nijar, Ya Sa Labule da Shugaba Bazoum

  • Gwamna Babagana Umaru Zulum na jihar Borno, ya kai ziyara ƙasar Nijar, inda ya amsa gayyatar da aka masa
  • Gwamnan ya gana da shugaban ƙasar Nijar, Muhammadu Bazoum, da gwamnan Diffa, Isa Lameen
  • An gudanar da wannan taro ne a garin Diffa, inda shugabannin suka tattauna kan yadda za'a maida yan gudun hijira

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umaru Zulum, yanzun haka yana ƙasar Nijar bisa amsa gayyatar shugaban ƙasa, Muhammad Bazoum.

Shugaba Bazoum ya karɓi bakuncin gwamna Zulum tare da tawagarsa da suka haɗa da Kakakin majalisar dokokin jihar Borno, Abdulkareem Lawan da Sanata Abubakar Kyari, inda suka shiga taron sirri a garin Diffa.

KARANTA ANAN: Wasu Fusatattun Mata da Ƙananan Yara Sun Toshe Hanyar Sokoto-Gusau

Taron ya maida hankali ne kan yan gudun hijira, waɗanda suka baro ƙauyukansu daga sassa daban-dabn na jihar Borno tun shekarar 2014, saboda yawaitar hare-haren yan Boko Haram.

Gwamna Zulum da Shugaba Bazoum
Da Ɗuminsa: Gwamna Zulum Ya Dira Ƙasar Nijar, Ya Sa Labule da Shugaba Bazoum Hoto: Governor Of Borno FB fage
Asali: Facebook

An fara taron ne jim kaɗan bayan gwamna Zulum da takwaransa na Diffa, Gwamna Lameen sun tarbi shugaba Bazoum a filin tashi da saukar jiragen sama na Tanja Momadou dake garin Diffa.

Garin Diffa na kusa da yankuna da dama na arewacin jihar Borno, yayin da garuruwa da dama a Borno suka haɗa iyaka da garin Diffa.

Zulum ya yi jawabi ga manema labarai bayan taron

Gwamna Zulum ya zanta da manema labarai jim kaɗan bayan fitowa daga taron. Hakan na ƙunshe ne a wani rubutu da gwamnan yayi a shafinsa na facebook.

Gwamnan yace: "Mun cimma abubuwa da dama a taron, Mun ɗauki wasu matakai da suka haɗa da maida yan asalin jihar Borno zuwa garuruwansu."

"Waɗannan mutanen sun ɗauki tsawon shekaru 6 a Nijar, Amma sabida cigaban da muka samu a ɓangaren tsaro, yanzun mutanen sun ƙosa su koma gidajensu."

"Zamu yi iyakar bakin ƙoƙarin mu wajen ganin mutanen mu sun koma ƙauyukansu cikin ƙoashin lafiya."

KARANTA ANAN: Da Ɗuminsa: Yan Majalisa Sun Yi Fatali da Buƙatar Ɗage Dokar Hana Twitter

Waɗanda suka mara wa gwamna Zulum baya zuwa Nijar sun haɗa da, Sanata mai wakiltar Borno ta arewa, Abubakar Kyari, kakakin majalisar dokokin jihar Borno, Abdulkarin Lawan da kuma wasu ƙusoshin gwamnatin jihar.

A wani labarin kuma Matawalle Ya Yi Magana Kan Kisan Ɗan Majalisar Jiharsa, Ya Bayyana Alhininsa

Gwamnan Zamfara, Bello Matawalli, ya yi jimamin kisan da aka yiwa ɗan majalisar dokokin jiharsa, Hon. G. Ahmed.

Gwamnan yayi ta'aziyya ga iyalan mamacin tare da addu'ar neman samun rahamar ubangiji.

Asali: Legit.ng

Online view pixel