Gwamnatin Kaduna ta yi magana kan zanga-zangar da ɗalibai suka yi a Kwalejin Gidan Waya

Gwamnatin Kaduna ta yi magana kan zanga-zangar da ɗalibai suka yi a Kwalejin Gidan Waya

  • Gwamnatin jihar Kano ta ce tana jiran rahotanni daga sojoji, yan sanda, DSS, kungiyar dalibai da wasu kafin yin tsokaci kan lamarin
  • Gwamnatin na Kaduna ta kuma ce rahotannin da ke cewa ta tura jami'an tsaro su hana a yi zanga-zangar ba gaskiya bane
  • Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya mika sakon ta'aziyya ga iyalan dalibin da ya rasu ya kuma yi wa wadanda jikkata fatan samun sauki

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce tana jiran cikaken rahoto a kan zanga-zangar da daliban Kwallejin Ilimi na Gwamnatin Kaduna da ke Gidan Waya suka yi.

Sanarwar da kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya fitar a shafinsa na Facebook a ranar Litinin ya ce a halin yanzu rahoton da gwamnati ta samu shine dalibi daya ya rasu, wasu sun jikkata sannan jami'an tsaro uku sun samu rauni.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Kaduna, Samuel Aruwan
Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na Kaduna, Samuel Aruwan. Hoto: Samuel Aruwan
Asali: UGC

DUBA WANNAN: 'Yan majalisar Zamfara baki ɗayansu za su bi Matawalle zuwa jam'iyyar APC, Hadimin Gwamna

Gwamnati ba ta tura jami'an tsaro su hana zanga-zanga ba

Har wa yau gwamnatin na jihar Kaduna ta ce bata tura jami'an tsaro domin su hana zanga-zangar ko musgunawa daliban da ke yin ta ba.

Gwamnatin jihar Kadunan ta kuma karyata rahotannin da ke cewa ta tura jami'an tsaro su musgunawa masu yin zanga-zangar.

KU KARANTA: Fastocin takarar shugaban ƙasa na Gwamna Bala Mohammed sun mamaye birnin Kano

Aruwan ya ce:

"Gwamnatin jihar Kaduna na jiran rahoto domin ta fahimci abin da ya haifar da rikicin da ya faru a Gidan Waya.
"A lokacin fitar da wannan sanarwar, Gwamna na jiran rahoto daga sojoji, yan sanda, DSS da mahukunta a makarantar, kungiyar dalibai da kuma masu sarautun gargajiya a yankin."

Ya kara da cewa gwamnatin za ta bayyana abin da ta gano bayan samun cikaken rahoton.

Gwamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai ya mika sakon ta'aziyya ga iyalan dalibin da ya rasa ransa yana kuma yi wa sauran daliban da jami'an tsaro fatan samun sauki cikin gaggawa.

A baya, mun kawo muku cewa an bindige dalibin kwallejin Iimi na Gidan Waya da ke karamar hukumar Jema'a a jihar Kaduna har lahira kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Marigayin yana zanga-zanga ne tare da yan uwansa dalibai da suka fito domin nuna rashin amincewarsu da karin kudin makaranta da gwamnatin jihar ta yi a baya bayan nan, amma sai jami'an tsaro suka zo suna kokarin tarwatsa su.

Wani daya daga cikin masu zanga-zangar da ya yi magana da Daily Trust amma ya nemi a sakaya sunansa ya ce sun fito ne su nuna kin amincewarsu da karin kudin makaranta da aka yi kawai sai suka hadu da jami'an tsaron a waje.

Asali: Legit.ng

Online view pixel