Daga Malam Daurawa: Mutane 12 da Zasu Iya Shan Azumi a Ramadana

Daga Malam Daurawa: Mutane 12 da Zasu Iya Shan Azumi a Ramadana

- Watan Azumin Ramadana wata ne mai falala da ake azumtar kwanaki 30 a jere ba ci ba sha da rana

- Azumi na da hukunce-hukunce, ciki har da wadanda suke magana kan ajiye Azumin ko yinsa

- Malamin addinin Islama, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana wasu hukunce-hukuncen yin Azumin

Azumin watan Ramadana na daga cikin ibadun da aka wajabta wa Musulmai, sai dai akwai wasu mutane 12 da aka ba su damar ajiye azumin, ko da yake hukunce-hukuncensu sun bambanta.

A wani bidiyo da BBC Hausa ta wallafa, daya daga cikin malaman addinin Musulunci a Najeriya Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana wasu mutune 12 da aka yi musu uzurin su ajiye azumi a watan Ramadana.

A cewar sa, wasu daga cikin mutanen za su rama Azumin, wasu kuwa ciyarwa za su yi, yayin da wasu ba za su ciyar ba kuma ba za su yi ramuwa ba.

Kara karanta wannan

Tsohon sarki Sanusi ya fadi karamcin da Wigwe ya yi masa da Ganduje ya tsige shi

KU KARANTA: Za Ku Yi Matukar Nadama Idan Aka Sauke Dr Pantami, Gumi Ga ’Yan Najeriya

Daga Malam Daurawa: Mutane 12 da zasu iya shan Azumi a Ramadana
Daga Malam Daurawa: Mutane 12 da zasu iya shan Azumi a Ramadana Hoto: bbc.com
Asali: UGC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wadanda za su rama Azumi:

1. Mace mai jinin al'ada

2. Matar da ta sha Azumi saboda jinin biki

3. Matafiyi

4. Mara lafiya

Wadanda za su ciyar:

5. Mace mai ciki

6. Mace mai shayarwa

7. Mai ciwon kishirwa

8. Mai ciwon 'yunwa

Wadanda ba za su rama ba, kuma ba za su ciyar ba:

9. Yaro

10. Mahaukaci

11. Tsofaffi

12. Mai ciwon farfadiya

KU KARANTA: Osinbajo Ya Bayyana Hasashensa Ga Ci Gaban Najeriya, Ya Ce Za a Samu Zaman Lafiya

A wani labarin, Shugaban Mabiya Shi’a na Kungiyar Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya (IMN), Sheikh Ibraheem Zakzaky ya raba kayan abinci na miliyoyin Nairori ga mabukata albarkacin watan Azumin Ramadan, Aminiya ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Tsohon sarkin Kano, Sanusi ya fashe da kuka a wajen makokin Herbert Wigwe, bidiyo

Dan sa Muhammad Ibraheem Zakzaky ne ya jagoranci shirin rabon kayan abincin da suka hada da buhunan Shinkafa da Sukari da Masara da Gero a madadin mahaifin nasa.

Awata takarda da ya sanya wa hannu, Muhammad Ibraheem Zakzaky ya ce mahaifin nasa ya bayar da umarnin rabon kayan Azumin ne ga mabukata.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel