Zan dafa wa mijina abinci sau uku a rana, wata budurwa ta sanar da mata masu tsatsauran ra’ayi

Zan dafa wa mijina abinci sau uku a rana, wata budurwa ta sanar da mata masu tsatsauran ra’ayi

- Wata budurwa ta je shafin soshiyal midiya don bayyana yadda za ta dauke dawainiyar mijinta a gidan aurenta

- A bisa ga wallafarta, ta bayyana cewa za ta girkawa mijinta abinci sau uku a rana sai dai idan shi yace ta huta

- Wallafar tata ta haddasa cece-kuce a tsakanin masu amfani da shafin zumunta

Wata yar Najeriya mai amfani da shafin Twitter @xarah_bint ta haddasa cece-kuce a shafin soshiyal midiya bayan ta bayyana kudirinta na daukar dawainiyar mijinta.

A wani wallafa da ta yi kai tsaye zuwa ga mata masu tsatsauran ra’ayi kan maza, ta bayyana cewa za ta dunga girkawa mijinta abinci sau uku a rana.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Gwamnatin Zamfara ta tabbatar da sace dalibai mata da yan bindiga suka yi

Zan dafa wa mijina abinci sau uku a rana, wata budurwa ta sanar da mata masu tsatsauran ra’ayi
Zan dafa wa mijina abinci sau uku a rana, wata budurwa ta sanar da mata masu tsatsauran ra’ayi hoto: @teezar_fashion
Asali: Instagram

A kalamanta:

“Na zo nan domin na tunatar da wadannan yan mata masu tsatsauran ra’ayi cewa zan dunga girkawa mijina abinci sau uku a kulla-yaumin har sai dai idan shi ya zabi ya bari na huta.”

Kalli wallafarta a kasa:

Kalli sharhin masu amfani da shafin soshiyal midiya a kasa:

theaprokoroom:

“Har sai dai idan shi ya zabi ki huta? Ina fatan zai maki kamar yadda kike yi mai.”

callmemjay:

“Kina iya mayar da shi sau 4 a rana.”

priscaberry_perfumes:

“Ina taya ki murna uwar-girki! Zabinki ne, babu ruwanmu a ciki♂️‍♀️‍♀️"

tdemuren:

“Yanzu ki je ki karbi lambar yabonki...sannu da kokari!”

KU KARANTA KUMA: Dalla-dalla: Yadda za a samu tallafin bashin FG ga masu kananan sana'o'i

gracemaryenenche:

“Girka, kina iya girkawa makwantankin ma.”

mercy__silvanus:

“Zabinki ♀️. Duk da yadda na kai da son girki, ba zan girkawa kaina abinci sau 3 a rana ba.”

A wani labarin, gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, a ranar Alhamis ya kai ziyara garin Dikwa inda ya rabawa al'ummar garin 34,000 kayan masarufi da kansa.

Mai magana da yawunsa, Malam Isa Gusau, ya bayyana hakan a jawabin da ya saki ranar Alhamis, 25 ga Febrairu, 2021.

A cewarsa, gwamnan ya raba kayan masarufi daban-daban ga iyalai 34,00.

Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai.

Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi.

Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara.

Don samun karin bayani a kan ta, ziyarci shafinta na Twitter @ AishaMu11512411

Asali: Legit.ng

Online view pixel