Da duminsa: An fara yi wa mutane jabun rigakafin Korona

Da duminsa: An fara yi wa mutane jabun rigakafin Korona

- NAFDAC ta gargadi ‘yan Najeriya da su kiyaye kansu dangane da rigakafin Korona na bogi

- Hukumar ta gano cewa an samu yaduwar allurar rigakafin Korona a wasu sassan kasar

- Hukumar ta kirayi gwamnati da sauran hukumomi cewa kada su fara yin allurar ba tare da amicewar NAFDAC ba

Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC) a ranar Juma’a ta bayyana cewa ba ta amince da duk wani rigakafin COVID-19 ba, The Nation ta ruwaito.

Ta yi gargadin alluran rigakafin bogi sun fara yawo a cikin kasar, inda ta yi kira ga jama'a da kar su sayi irin wadannan magunguna domin suna iya haifar da cututtuka irin na COVID-19 kuma za su iya haifar da mutuwa.

Ta kuma bukaci cibiyoyin gwamnati, hukumomi da manyan kamfanoni da kada su yi odar allurar rigakafin ta COVID ba tare da tabbatarwa daga NAFDAC ba idan an amince da maganin.

KU KARANTA: Kuyi adalci wajen sukar da kukewa gwamnatina, Inji Buhari ga manyan kasa

An fara yi wa mutane rigakafin Korona na bogi
An fara yi wa mutane rigakafin Korona na bogi Hoto: The Guardian
Asali: Facebook

Darakta-Janar na NAFDAC, Farfesa Mojisola Adeyeye ce ta bayyana hakan a Abuja yayin wani taron tattaunawa da manema labarai.

Ta ce: “Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC) ba ta samu wani takaddama ba daga masana’antun da ke kera allurar ta Covid har yanzu saboda haka babu wani maganin da NAFDAC ta amince da shi.

“Alurar rigakafin ta Covid-19 sabuwa ce, kuma dole ne a sanya ido a kan illolin ko kuma abubuwan da za su haifar, don haka, idan NAFDAC ba ta amince da hakan ba, to bai kamata jama’a su yi amfani da shi ba.

“Akwai rahotannin yin allurar rigakafin karya a Najeriya. NAFDAC tana rokon jama'a da su kiyaye.

“Babu wani rigakafin Covid da NAFDAC ta amince dashi. Alluran rigakafin na iya haifar da cututtuka kamar na Covid ko wasu munanan cututtuka waɗanda zasu iya kisa.

“Bai kamata wani kamfani ko kamfani yayi odar allurar rigakafin ba. Kamfanonin da ke kera alluran idan kamfanoni na gaske ne sun san dole ne su gabatar da aikace-aikacen su ga NAFDAC.

KU KARANTA: Babu cutarwar da za ta sami Bishop Kukah - CAN

"Babu wasu cibiyoyin gwamnati ko hukumomin da za su ba da umarnin maganin Covid ba tare da tabbatarwa daga NAFDAC ba idan an amince da allurar."

A wani labarin, Tawagar masana daga Hukumar Lafiya ta Duniya sun isa Wuhan ranar Alhamis don yin bincike kan asalin cutar COVID-19 fiye da shekara guda bayan fitowarta, yayin da Sin ta ba da rahoton mutuwa ta farko daga Covid-19 watanni takwas da suka gabata.

Jaridar The Punch ta ruwaito cewa, masana kimiyya 10 sun sauka ne saboda aikin da suka jinkirta sosai, sun hadu da jami'an kasar Sin a cikin kayan hazmat yayin da su ma a ka basu kayan kariyan.

An kai jami'an wani otal domin zaman jira na makwanni 2 kamar yadda dokar COVID-19 ta tabbatar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel