Babbar Magana: Akwai yiyuwar barkewar sabon yajin aiki a Jami'o'i

Babbar Magana: Akwai yiyuwar barkewar sabon yajin aiki a Jami'o'i

- Kungiyar NAAT ta buqaci a fayyace adadin kudade da za a ba wa kungiyar daga kudaden da gwamnati ta saki wa kungiyoyin jami'o'i

- Kungiyar ta nuna rashin amincewarta da yadda ASUU suka shirya kasafta kudin

- Shugaban kungiyar ya zayyana yadda sukai alkawari da gwamnati a kan yadda za a raba kudin

Kungiyar masana ilimin kimiyya (NAAT) ta bayar da sanarwar yajin aiki na kwanaki 14 ga Gwamnatin Tarayya.

Ma’aikatan jami’ar suna zanga-zangar nuna rashin bambanci ne a kan raba Naira biliyan 40 da aka samu ga kungiyoyin ma’aikatan jami’o’i hudu, The Punch ta ruwaito

Suna kuma neman a saki 50% cikin 100% na Naira biliyan 71 da aka tara na alawus-alawus da suke bin mambobin kungiyar bisa yarjejeniyar da suka yi da gwamnatin a shekarar 2009.

KU KARANTA: Aisha Yesufu ta caccaki gwamnatin Buhari a kan kama Sowore

Babbar Magana: Akwai yiyuwar barkewar sabon yajin aiki a Jami'o'i
Babbar Magana: Akwai yiyuwar barkewar sabon yajin aiki a Jami'o'i Hoto: Facebook/Sun News
Asali: Facebook

Shugaban NAAT, Ibeji Nwokoma, ya fadawa manema labarai a Abuja ranar Asabar, cewa kungiyar ta rubutawa Ministan kwadago da samar da ayyuka, Sanata Chris Ngige, inda ta sanar da shi shirin da suke shirin yi na masana'antu.

Ya ce, “Mun rubuta wa gwamnati cewa ya kamata a ba NAAT a matsayinta kungiya wani kaso na N40bn. Dole ne ku ayyana shi; ba za ku iya cewa ASUU 75?% cikin ɗari wasu 25% cikin ɗari ba. Bari mu san takamaiman kason da zaku baiwa NAAT a matsayin ƙungiya.

KU KARANTA: Allurar rigakafin COVID-19: Damuwa kan Sayen ta, Adana ta da Gudanar da ita

"A cikin MoU da muka shiga tare da gwamnati a ranar 18 ga Nuwamba, a cikin lamba 2b, mun bukaci a raba N40bn da aka saki, cewa gwamnati ya kamata a fayyace a fili abin da za a kasaftawa kowace kungiya kuma gwamnati ta amince da gaskiyar bukatun mu kuma ya ce NUC (Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa) da kuma Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya za su yi aiki tare tare da kungiyar kwadago kuma abin da suka yi ya saba wa akidar MoU din gaba daya.”

A wani labarin, Kungiyar malamai masu koyarwa na jami'o'i (ASUU) a ranar Talata, 22 ga watan Disamban 2020, ta bada satar amsa a kan lokacin da za ta kawo karshen yajin aikinta na watanni 9.

Kungiyar ta sanar da hakan a wata wallafa da tayi a shafinta na Twitter.

Kamar yadda wallafa ta ce: "Labari mai dadi. Za a janye yajin aiki idan har gwamnatin tarayya ta biya dukkan albashin da malamai ke bin ta."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel