Yanzu Yanzu: Shahararren malamin Musulunci a Nigeria Sheikh Ahmed Lemu ya rasu

Yanzu Yanzu: Shahararren malamin Musulunci a Nigeria Sheikh Ahmed Lemu ya rasu

- Fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmed Lemu, ya rasu

- Sheikh Lemu ya rasu ne da sanyin safiyar yau Alhamis, 24 ga watan Disamba

- Marigayin ya yiwa addinin Musulunci sosai a lokacin da yake raye

Allah ya yiwa shahararren malamin nan na addinin Musulunci da ke Najeriya, Sheikh Ahmed Lemu rasuwa.

Shehin malamin ya rasu ne a safiyar yau Alhamis, 24 ga watan Disamba a garin Minna, babbar birnin jihar Niger.

Ya rasu yana da shekara 91 a duniya.

Yanzu Yanzu: Shahararren malamin Musulunci a Nigeria Sheikh Ahmed Lemu ya rasu
Yanzu Yanzu: Shahararren malamin Musulunci a Nigeria Sheikh Ahmed Lemu ya rasu Hoto: Kingfaisalprize.org
Asali: UGC

Daya daga cikin yayan marigayin, Maryam Lemu, ta tabbatar da mutuwar mahaifinsu a wata sanarwa a Facebook, ta ce idan anjima kadan za a soma shirye-shiryen binne shi.

Sheikh Dr. Lemu shahararren masani, ya kasance mutum ne da ya sadaukar da rayuwarsa ga yiwa musulunci hidima.

KU KARANTA KUMA: Wasu yan siyasa na yi wa Buhari bita da kulli, fadar shugaban kasa

Hakazalika mutum ne mai kira ga yin masalaha da sassauci a tsakanin al'umma da kuma bayyana ra'ayinsa akan al'amura ba tare da rufa-rufa ba.

Sheikh Lemu ya bada muhimmiyar gudunmawa wajen kare hakkin mata, haka kuma ya kafa kungiyar Da'awa domin yaki da tsattsauran ra'ayi.

A wani labarin, mun ji cewa mutanen garin Azare a jihar Bauchi sun shiga alhini sakamakon mutuwar Sarkin Dawakin Katagum, Alhaji Muhammad Lele Mukhtar.

Mukhtar, wanda ya kasance tsohon sakataren dindindin na tarayya ya rasu ne a ranar Talata, 22 ga watan Disamba.

Marigayin basaraken ya yi aiki a matsayin kwamishina na kasa, hukumar tsare-tsare ta kasa (NPLC) kuma mamba a majalisar FJSC.

A gefe guda kuma, Usman Faruk, gwamna na farko a mulkin soja a jihar arewa maso yamma, ya rasu, lamarin da ya jefa Gombe cikin halin juyayi.

Tsohon gwamnan na mulkin soja ya rasu a ranar Juma’a, 18 ga watan Disamba.

Ya yi aiki a matsayin gwamna a mulkin soja a jihar ta arewa maso yamma daga 1967 zuwa 1975 bayan an wareta daga tsohuwar yankin arewa a mulkin soja na Janar Yakubu Gowon.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng