Korona: Kasashe 48 sun haramta shigowa daga Ingila kan hauhawan masu cutar

Korona: Kasashe 48 sun haramta shigowa daga Ingila kan hauhawan masu cutar

- Akalla kasashe 45 ne suka dakatar da jiragen sama daga Ingila yayinda kasar ke samun karuwar wadanda suka kamu da cutar korona a sabon rukunin bullar ta

- An tattaro cewa wani sabon rukuni na annobar ya karade fadin kudancin Ingila

- Channels TV ta ruwaito cewa tuni Scotland ta rufe iyakarta da sauran Ingila

Legit.ng ta ruwaito cewa kwamitin fadar Shugaban kasa kan COVID-19 a ranar Litinin, 21 ga watan Disamba, ya ce hukumomin Najeriya na sane da kira ga haramta tafiye-tafiyen kasashen waje sakamakon gano barkewar cutar a wasu kasashe.

Boss Mustapha, Shugaban kwamitin PTF kuma sakataren gwamnatin tarayya, ya yi bayanin cewa kwamitin da hukumomin jiragen sama da na lafiya, ciki harda kungiyar lafiya ta duniya (WHO), na zuba idanu sosai kan lamarin.

KU KARANTA KUMA: Lele Mukhtar, tsohon sakataren tarayya kuma Sarkin Dawakin Katagum, ya rasu

Korona: Kasashe 48 sun haramta shigowa daga Ingila kan hauhawan masu cutar
Korona: Kasashe 48 sun haramta shigowa daga Ingila kan hauhawan masu cutar Hoto: Gareth Fuller
Asali: Getty Images

Ga wasu daga cikin kasashen da suka haramta shigowa daga Ingila a kasa:

1. France

2. Germany

3. Spain

4. Portugal

5. India

6. Poland

7. Hong Kong

8. the Netherlands

9. Ireland

10. Italy

11. Russia

12. Finland

13. Austria

14. Switzerland

15. Baltic nations Estonia,

16. Latvia

17. Lithuania

18. Hungary

19. Luxembourg

20. Balkans

21. Croatia

22. Macedonia

23. Albania

24. Bulgaria

25. Romania

26. the Czech Republic.

27. Norway

28. Sweden

29. Denmark

30. Belgium

31. Canada

32. Turkey

33. South Africa.

34. Saudi Arabia

35. Oman

36. Israel

37. Jordan

38. Kuwait

39. Morocco

40. Algeria

41. Tunisia

42. Mauritius PAY ATTENTION

43. Latin America

44. Panama

45. Paraguay

46. Peru

47. Chile

48. Argentina

KU KARANTA KUMA: Yan bindiga sun sace basarake da wasu mutum 15 a kauyen Katsina

A wani labarin, FG ta fara nazari a kan yiwuwar sake rufe iyakokin kasar bayan budeta da tayi a kwanan nan.

Gwamnatin tarayyar ta ce za ta dauki matakin sake rufe iyakokin ne idan har matsalar rashin tsaro ya ci gaba.

A yan baya bayan nan ne kasar ta fuskanci yawan hare haren ta'addanci daga wasu miyagu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel