Kwayar cutar B.1.1.7 lineage ta bayyana a Osun inji Shugaban cibiyar ACEGID

Kwayar cutar B.1.1.7 lineage ta bayyana a Osun inji Shugaban cibiyar ACEGID

- Masana sun ce an fara samun masu dauke da kwayar SARS-CoV-2 a Najeriya

- Africa Centre of Excellence for Genomics of Infectious Diseases ta gano wannan

- Shugaban cibiyar binciken yace N501Y, A570D da HV 69 – 70 ba su bayyana ba

Jaridar Premium Times ta fitar da rahoto cewa sabuwar nau’in Coronavirus da yanzu haka ya ke tada hankalin al’umma ya bayyana a Najeriya.

Kwararrun masanan da ke aiki da cibiyar bincike kan cututtuka masu yaduwa a Afrika ta jami’ar Redeemers-Ede, Osun, su ka tabbatar da wannan.

Ana yi wa sabon nau’in COVID-19 wanda aka gano a Ingila a watan Satumba lakabi da lineage B.1.1.7.

A wani rubutu da masanan da ke aiki da wannan cibiya ta ACEGID su ka fitar a shafin Virological, sun yi ikirarin ganin cutar a jikin mutane a Osun.

KU KARANTA: Tambayoyi da amsa game da maganin COVID-19

Masanan sun ce sun fara ganin cutar ne a jihar Osun a jikin wani da aka dauki jininsa a Agusta. A watan Oktoba, aka sake ganin da cutar a jikin wani.

A dalilin barkewar cutar ne kasashen Duniya da-dama su ka sa takunkumin hana shiga Ingila, sannnan su ka hana mutanen yankin zuwa kasarsu.

Shugaban cibiyar bincike ta ACEGID, Farfesa Christian Happi wanda ya kware sosai a kan wannan harka ya ce sun ga B.1.1.7 lineage a Najeriya.

Duk da karuwar cutar COVID-19 da ake samu, Farfesan ya ce kawo yanzu 1% na masu jinya a Najeriya ne su ka kamu ta kwayar cutar SARS-CoV-2.

KU KARANTA: Uwargidar Najeriya Aisha Buhari ta tafi Dubai neman magani

Kwayar cutar B.1.1.7 lineage ta bayyana a Osun inji Shugaban cibiyar ACEGID
Shugaban PTF, Sani Aliyu Hoto: nairametrics.com
Asali: UGC

Masanin ya kuma bayyana cewa sauran nau’ukan COVID-19 irinsu N501Y, A570D, da HV 69 – 70, ba su kai ga bayyana a jikin mutanen kasar ba tukun.

Tun a jiya ku ka ji cewa sabuwar kwayar COVID-19 ta fara tsorata gwamnatin Najeriya, har an kai ga tunanin lafta takunkumi domin dakile yaduwar cutar.

Barkowar samfurin Coronavirus na SARS-CoV-2 ya sa kasashe sun daina zirga-zirga zuwa Ingila, inda irin wannan kwayar cuta ya fara bayyana kwanaki.

Gwamnatin Tarayya ta ce COVID-19 da ta dawo ta na da ban tsoro, dole a firgita da irin hadarinta.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel