'Yan sanda sun kashe masu garkuwa da mutane 2, sun cafke 'yan fashi a Sokoto

'Yan sanda sun kashe masu garkuwa da mutane 2, sun cafke 'yan fashi a Sokoto

- An kashe wasu mutane 2 da ake zargin 'yan fashi ne a karamar hukumar Tambuwal dake jihar Sokoto

- Sannan 'yan sandan sun samu nasarar damkar wasu masu garkuwa da mutane guda 8

- An samu bindigogi kirar AK-47 a hannunsu, da kuma sauran miyagun makamai

An kashe wasu mutane 2 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a wuraren Sanyinna da ke karamar hukumar Tambuwal a jihar Sokoto, yayin harbe-harbe da 'yan sanda.

Kwamishinan 'yan sanda, Ibrahim Sani Ka'oje ya bayyana hakan a ranar Asabar a wani taro da suka yi a hedkwatar 'yan sanda, Channels TV ta wallafa.

Kamar yadda yayi bayani, ana zargin daya daga cikinsu da fashi da makamai a sati 2 da suka wuce, inda ya kashe mutane 2 a wuraren Tamaje da ke jihar, amma an damke shi.

Fashi 4 da aka yi, wanda aka kama mutane 8 da ake zargin 'yan fashi ne da miyagun makamai. Garin hakan ne aka amshi AK-47 da sauran miyagun makamai daga hannunsu.

KU KARANTA: 2023: Jigo a APC ya bayyana mutanen da za su fitar da yankin shugaban kasa

'Yan sanda sun kashe masu garkuwa da mutane 2, sun cafke 'yan fashi 2 a Sokoto
'Yan sanda sun kashe masu garkuwa da mutane 2, sun cafke 'yan fashi 2 a Sokoto. Hoto daga @ChannelTV
Asali: Twitter

KU KARANTA: Bidiyon soja yana dukan budurwa tare da yi mata tsirara a titi kan shigar banza

A wani labari na daban, wata yarinya ta koma sana'ar tukin keke-Napep don kulawa da kanninta da kuma biyan basukan da ake bin mahaifnta da ya mutu.

Wata Kaothar Ajani, mai shekaru 16, ta zage wurin sana'ar tukin Keke-Napep bayan mutuwar mahaifinta. Tana sana'ar ne don kulawa da kanta da mahaifiyarta.

A al'adar Afirika, akwai ayyuka daban-daban wadanda aka saba maza ne suke yi, ba haramun ne mata su yi ba, amma kuma maza ne suka yi fice a sana'o'in.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel