Ka fito da kanka don kare Ndume daga wannan tozarcin, dan uwan Maina ya roke shi

Ka fito da kanka don kare Ndume daga wannan tozarcin, dan uwan Maina ya roke shi

- Aliyu Maina, dan uwan tsohon shugaban hukumar fansho, Abdulrasheed Maina, ya roki kawunsa a kan ya mika kansa ga yan sanda

- Maina na fuskantar shari’a a kan almubazaranci da kudaden fansho

- An tsare Sanata Aliyu Ndume wanda ya tsaya wa Maina a matsayin jingina a gidan maza, a ranar Litinin, 23 ga watan Nuwamba

Kwanaki biyu bayan babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tsare sanata mai wakiltan Borno ta Kudu, Ali Ndume a gidan yari kan rashin gabatar da Abdulrasheed Maina a kotu, dan uwan tsohon Shugaban hukumar ta fansho, Aliyu Maina ya yi martani.

Aliyu ya bukaci kawun nasa a kan ya gabatar da kansa ga rundunar yan sanda.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa Aliyu ya ce sake bayyanar Maina zai dakatar da tozarcin da Ndume ke fuskanta a idon duniya kafin lamarin ya tabarbare.

Ka fito da kanka don kare Ndume daga wannan tozarcin, dan uwan Maina ya roke shi
Ka fito da kanka don kare Ndume daga wannan tozarcin, dan uwan Maina ya roke shi Hoto: EFCC
Asali: Facebook

KU KARANTA KUMA: Hariji kuma matsafi: Kotu ta raba auren mijin da ke saduwa da matarsa tsawon awanni

Legit.ng ta tattaro cewa Aliyu, dan uwan Maina na kut-da-kut, ya ce sanata Ndume ya azabtu sosai a kan Maina.

Ya kara da cewa abun bakin ciki ne ganin cewa yana biyan bashi don kawai ya taimaki dan mazabarsa.

Aliyu ya yi kira ga Maina a kan ya taimaki halin da ake ciki, cewa tserewar na kara tabarbarar da shari’arsa ne, sannan cewa ya gabatar da kansa don a samu damar kawo karshen al’amarin.

Ya ce:

“Na yi magana da Sanata Ndume da wasu hadimansa lokuta da dama kuma na basu tabbacin cewa Maina zai gurfana a gaban kotu da zaran ya warke, amma abun bakin ciki, ya ki aikata hakan. Ban sanya idanu a kansa ba tsawon watanni uku yanzu domin yana gudun kowa.”

KU KARANTA KUMA: Hukumar kurkukun Kuje ta saka takunkumi, ta hana 'yan majalisa ganin Ndume

A gefe guda, Kungiyar matasan Arewa , ta yi Allah wadai da tsare sanata mai wakiltar Borno ta Kudu, Ali Ndume, bisa yadda ya kasa gabatar da Abdulrasheed Maina.

Maina ya gudu daga beli akan almundahanar kudi Naira biliyan 2 kamar yadda Legit.ng ta ruwaito.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng