Yadda yan bindiga suka tarwatsa wani kauye a jihar Zamfara

Yadda yan bindiga suka tarwatsa wani kauye a jihar Zamfara

- Mazauna kauyen Aljumma a jihar Zamfara sun shiga dimuwa bayan wani harin yan bindiga a ranar Lahadi

- An tattaro cewa maharan sama da guda 50 sun kai farmaki kauyen a saman babura inda suka fara harbe-harbe

- Jami’an tsaro sun yi nasarar dakile harin da fari amma kuma sai maharan suka sake dawowa lamarin da ya sanya mazauna yankin tarwatsewa don tsira

Al’umman kauyen Aljumma da ke karamar hukumar Maradun na jihar Zamfara sun bayyana cewa yan bindiga sun tarwatsa su bayan wani hari da suka kai masu a ranar Lahadi.

Sashin Hausa na BBC ta ruwaito cewa wani mazaunin kauyen ya sanar da ita cewa yan bindigar fiye da 50 sun kai farmaki kauyensu a kan babura sannan suka bude wuta.

Amma kuma ya bayyana cewa jami’an tsaro da yan banga sun yi nasarar fatattakarsu amma sai suka sake dawowa daga bisani, lamarin da ya gigita mazauna kauyen har suka shiga daji don tsiratar da rayuwarsu.

Yadda yan bindiga suka tarwatsa wani kauye a jihar Zamfara
Yadda yan bindiga suka tarwatsa wani kauye a jihar Zamfara Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

KU KARANTA KUMA: Za mu farauto makasan Shugaban APC na Nasarawa, Gwamna Sule ya sha alwashi

Ya bayyana cewa: “mutanen gari na tserewa mata da kananan yara.”

Lamarin na zuwa ne bayan 'yan bindiga sun afka masallacin Juma'a a kauyen Dutsin Gari a Kanoma, Jihar Zamfara a ranar Juma'a, inda suka yi awon gaba da liman da masallata kimanin guda 40.

Kauyen da ya yi suna saboda noman rake yana fuskantar hare-haren 'yan bindiga a baya bayan nan.

Kwararran majiyoyi a kauyen sun shaidawa Daily Nigerian cewa maharan da suka taho a kan babura fiye da 100 sun kashe masallata 5 sannan suka raunta da dama.

Majiyoyin sun ce harbe-harben da 'yan bindigan da suka yi yayin da suka isa masallacin Juma'an ya janyo turereniya bayan liman ya yanke salla a raka'a na farko.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng