'Yan bindiga sun kashe masallata 5, sunyi awon gaba da liman da mutum 40 yayin sallar Juma'a a Zamfara

'Yan bindiga sun kashe masallata 5, sunyi awon gaba da liman da mutum 40 yayin sallar Juma'a a Zamfara

- 'Yan bindiga sun kai hari masallacin Juma'a a kauyen Dutsin Gari a Kanoma Jihar Zamfara

- 'Yan bindigan sun kashe mutane biyar bayan sun bude wuta wadda hakan yasa liman ya datse sallar

- Sun yi garkuwa da liman da wasu mutum 40 amma sun sako limanin da wasu cikin mutanen a ranar Asabar

'Yan bindiga a ranar Juma'a sun afka masallacin Juma'a a kauyen Dutsin Gari a Kanoma, Jihar Zamfara sun yi awon gaba da liman da masallata kimanin guda 40.

Kauyen da ya yi suna saboda noman rake yana fuskantar hare-haren 'yan bindiga a baya bayan nan.

'Yan bindiga sun kashe masallata 5, sun sace liman da mutum 40 yayin sallar Juma'a a Zamfara
'Yan bindiga sun kashe masallata 5, sun sace liman da mutum 40 yayin sallar Juma'a a Zamfara. Hoto: @daily_nigerian
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: An kama mutum biyu bisa zargin cin babbakakken naman 'yan sanda

Kwararran majiyoyi a kauyen sun shaidawa Daily Nigerian cewa maharan da suka taho a kan babura fiye da 100 sun kashe masallata 5 sannan suka raunta da dama.

Majiyoyin sun ce harbe-harben da 'yan bindigan da suka yi yayin da suka isa masallacin Juma'an ya janyo turereniya bayan liman ya yanke salla a raka'a na farko.

'Yan bindigan sun yi awon gaba da limanin mai suna Mallam Yahaya da kimanin mutane 40 a kan babura suka shiga daji da su.

KU KARANTA: 'Na gwammace a datse min kai a maimakon in bada haƙuri', martanin Bashir El Rufai ga masu sukar hotunansa da Nwakaego

Wani mazaunin kauyen, Sani Kanoma ya shaidawa majiyar Legit.ng an sako limamin da wasu daga cikin masallatan daga baya a ranar Asabar.

Mista Kanoma ya ce bisa dukkan alamu 'yan bindigan sun zo ne don sace manoman rake masu arziki sosai wadanda suka biya miliyoyin naira a matsayin kudin fansa.

Da aka tuntube shi, mai magana da yawun rundunar 'yan sandan Zamfara, Mohammed Shehu ya ce zai bada cikaken bayani kan lamarin a ranar Lahadi.

A wani labarin, Gwamna Yahaya Bello na Jihar Kogi ya siffanta Shugaba Muhammadu Buhari a matsayin 'raɓa' a yayin da ya ke tsokaci a kan wani littafi da aka rubuta kan shugaban kasar mai taken "The Buhari in Us".

Yahaya Bello ya furta hakan ne cikin wani faifan bidiyo da ya bazu a shafunkan sada zumunta.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel