2023: Dattawan arewa sun goyi bayan shugabancin Igbo

2023: Dattawan arewa sun goyi bayan shugabancin Igbo

- Gabannin zaben 2023, ana ta kiraye-kiraye a kan goyon bayan shugabancin Igbo

- Kungiyar dattawan arewa masu son zaman lafiya da ci gaba na daya daga cikin masu goyon bayan Shugaban kasa dan kabilar Igbo

- Dattawan na arewa sun ce lallai ya kamata a mika tikitin Shugaban kasa na 2023 zuwa kudu maso gabas

Yayinda aka fara kamfen a kan zaben Shugaban kasa na 2023, kungiyar dattawan arewa masu son zaman lafiya da ci gaba sun fara goyon bayan shugabancin kabilar Igbo.

A wani rahoto da jaridar Leadership ta wallafa, dattawan arewan sun bayyana cewa lallai ya kamata a mika wa yankin kudu maso gabashin Najeriya shugabancin kasar a 2023 ba wani wani yanki daban ba.

Dattawan sun bayyana matsayinsu a cikin wata sanarwa daga shugabansu na kasa, Injiniya Zana Goni da Hajia Mario Bichi, shugabar mata ta kasa.

2023: Dattawan arewa sun goyi bayan shugabancin Igbo
2023: Dattawan arewa sun goyi bayan shugabancin Igbo Hoto: @APCNigeria
Asali: Twitter

Sun bayyana cewa ya kamata shugaban kasar na gaba ya kasance Igbo sannan sun bayar da shawarar cewa a ci gaba da tsarin tsarin karba-karba tsakanin arewa da kudu.

KU KARANTA KUMA: Rahoto ya yi ikirarin cewa ana zawarcin Jonathan kan ya fito takara a APC

A cewar dattawan arewan, mulkin karba-karba ya taimaka wajen rage tashin hankali a Najeriya.

Yayinda suke bayyana cewa matsayarsu ya fito ne daga bukatar son ganin an yiwa dukkanin yankunan Najeriya adalci a lamuran siyasar kasar, kungiyar dattawan sun ce a mayar da Igbo saniyar ware a tsarin yin abubuwa.

Dattawan sun yi kira ga jam’iyyun All Progressives Congress, (APC) da Peoples Democratic Party, (PDP), a kan su cike gurbin yan takara daga kudu maso gabas.

A bangare guda, dattawan na arewa sun roki dukkanin yankunan kasar a kan su marawa Igbo baya a fafutukarsu na son samar da Shugaban kasa.

KU KARANTA KUMA: Ziyarar gwamonin APC ga Goodluck Jonathan: PDP ta yi martani

A gefe guda, Ambasada Yahaya Kwande, jigon kungiyar dattawan arewa, ya nemi PDP ta mika tikitinta ga yankin arewacin kasar a 2023.

Jaridar Nigerian Tribune ta ruwaito cewa tsohon jakadan na Najeriya a kasar Switzerland, ya yi bayanin cewa tsarin karba-karba baya cikin gudun tsarin mulkin kasar, cewa tsari ne na jam’iyyun siyasa don magance wasu matsalolin da Najeriya ke fuskanta.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Tags: