Zamfara: Tsofin Kansiloli 69 tare da magoya bayansu sun sauya sheka zuwa PDP

Zamfara: Tsofin Kansiloli 69 tare da magoya bayansu sun sauya sheka zuwa PDP

- Wasu gungun tsofin kansiloli har su 69 tare da magoya bayansu sun dunguma sun koma jam'iyyar PDP a jihar Zamfara

- Jamilu Iliyasu, sakataren yada labaran gwamna Bello Matawalle, ya ce tsofin kansilolin sun yi mulki a tsakanin 2012 zuwa 2019

- Sauyin shekar kansilolin na zuwa ne a daidai lokacin da ake cece-kuce a kan komawar gwamna Dave Umahi na Ebonyi jam'iyyar APC

A kalla tsofin kansiloli 69 ne daga kananan hukumomi 14 a jihar Zamfara suka sauya sheka daga jam'iyyar APC zuwa PDP, kamar yadda Punch ta rawaito.

Hakan na kunshe ne a cikin wata takardar sanarwa da Jamilu Iliyasu, sakataren yada labaran gwamna Bello Matawalle, ya fitar a ranar Talata.

Ya ce tsofin kansilolin, wadanda suka yi mulki a tsakanin 2012 zuwa 2019, sun hada kansu a karkashin kungiya guda kafin su dunguma zuwa cikin jam'iyyar PDP.

KARANTA: Trump ya bayyana kansa a matsayin wanda ya lashe halastaccen zaɓe a Amurka

Shugaban kungiyar tsofin kansilolin, Tukur Magami, ya ce sun yanke shawarar komawa jam'iyyar PDP ne saboda gamsuwarsu da salon mulkin gwamna Matawalle.

Zamfara: Tsofin Kansiloli 69 tare da magoya bayansu sun sauya sheka zuwa PDP
Gwamna Bello Matawalle @Punch
Asali: Twitter

A cewarsa, gwamnati, irin ta Matawalle, mai kishin jama'a, ta na bukatar gudunmawa da goyon baya domin samun damar cigaba da ayyukan alheri.

KARANTA: 'Yan bindiga sun sace ASP 12 daga tawagar 'yan sanda a tsakanin Katsina da Zamfara

A nasa jawabin, Matawalle ya nuna jin dadinsa tare da yin Kira ga duk masu kishin Zamfara da jama'ar ta a kan su hada kai da shi domin ciyar da jihar gaba.

Sauyin shekar kansilolin na zuwa ne a daidai lokacin da ake cigaba da cece-kuce a kan ficewar gwamnan jihar Ebonyi, Dave Umahi, wanda ya sauya sheka zuwa jam'iyyar APC a cikin makon nan.

Legit.ng ta rawaito cewa Umahi, a ranar Talata, 17 ga watan Nuwamba, ya ce ya zama abun zargi a jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) saboda kawai ya ki caccakar Shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng