Yanzu Yanzu: Buhari na cikin ganawa da shugabannin tsaro a fadar Shugaban kasa
- Shugaban kasa Muhammadu Buhari na ganawa da shugabannin tsaro na kasa
- Mataimakin shugaban kasa, manyan jami'an gwamnati da wasu daga cikin ministoci duk sun hallara
- Sai dai babban mai ba shugaban kasa shawara kan tsaron kasa, Babagana Monguno bai isa dakin taron ba a yanzu haka
A yanzu haka, Shugaban kasa Muhammadu Buhari na jagorantar taron majalisar tsaro ta kasa, a fadar Shugaban kasa da ke Abuja.
Wadanda suka halarci taron sun hada da mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo; sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha; Shugaban ma’aikatan Shugaban kasa, Ibrahim Gambari.
Sai Atoni Janar na tarayya kuma ministan shari’a, Abubakar Malami da ministan tsaro, Manjo Janar Bashir Salihi Magaji (mai ritaya).

Asali: Twitter
Sauran da suka hallara sune ministan cikin harkokin cikin, Rauf Aregbesola; ministan harkokin waje, Geoffery Onyeama, da kuma ministan harkokin yan sandan, Muhammad Dingyadi.
KU KARANTA KUMA: Yanzu yanzu: Yan bindiga sun kashe Hakimin Gidan Zaki tare da mutane 3 a Kaduna
A daidai lokacin kawo wannan rahoton, babban mai ba kasa shawara a kan tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno (mai ritaya) wanda ya shirya taron bai hallara ba tukuna.
Shugabannin tsaro da suka hallara sune Shugaban ma’aikatan tsaro, Janar Gabriel Olonisakin; Shugaban hafsan soji, Laftanal Janar Tukur Buratai.
Sai kuma Shugaban sojin ruwa, Vice Admiral Ibok Ekwe-Ibas; da Shugaban hafsan sojin sama, Air Marshall Sadique Abubakar.
Sufeto Janar na yan sanda, IGP Mohammed Adamu; daraktan hukumar liken asiri na kasa; Ahmed Rafa’i Abubakar; da Darakta Janar na rundunar tsaro ta farin kaya (DSS), Yusuf Magaji Bichi ma sun hallara.
Ga hotunan ganawar wanda fadar shugaban kasa ta wallafa a shafinta na Twitter:
KU KARANTA KUMA: Covid-19: Yadda muka ciyar da iyalai 127,588 lokacin kulle - Minista Sadiya
A wani labari na daban, mun ji a baya cewa Shugaban majalisar wakilai ya yi ganawar sirri tare da shugabannin hukumomin tsaro a kasar.
Mataimakin kakakin majalisar wakilai, Ahmed Wase ne ya jagoranci ganawar wanda aka fara da misalin karfe 2:15 na yau Litinin, 16 ga watan Nuwamba, jaridar Punch ta ruwaito.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng