Wata mata sanye da hijabi ta yi garkuwa da wani yaro a Jigawa

Wata mata sanye da hijabi ta yi garkuwa da wani yaro a Jigawa

- Wata mata da ake zaton mai garkuwa da mutane ce ta badda kammani sanye da hijabi, sannan ta sace wani yaro a jihar Jigawa

- Rundunar yan sandan Jigawa ta tabbatar da faruwar lamarin

- An tattaro cewa masu garkuwa da mutanen sun saki yaron bayan mahaifinsa ya biya kudin fansa

Hankula sun tashi a jihar Jigawa lokacin da wata mata sanye da hijabi ta yi garkuwa da wani yaro dan shekara biyar mai suna Muhmad Tasiu, a Dutse, babbar birnin jihar.

Shaidu sun bayyana cewa yaron ya bata a ranar Lahadi, 15 ga watan Nuwamba, jim kadan bayan an gan shi tare da wata mata da ba a san ko wacece ba, jaridar Premium Times ta ruwaito.

KU KARANTA KUMA: Ba fa a mulkin soja muke ba; Buba Galadima ya kwankwashi Buhari a kan taba jagororin ENDSARS

Wata mata sanye da hijabi ta yi garkuwa da wani yaro a Jigawa
Wata mata sanye da hijabi ta yi garkuwa da wani yaro a Jigawa Hoto: @PremiumTimesng
Asali: UGC

Kakakin yan sandan jihar, Audu Jinjiri ya ce lamarin garkuwan ya afku ne a garin Galamawa.

Rundunar yan sandan ta ce:

“Daga bisani masu garkuwa da mutanen sun kira iyayensa inda suka bukaci a biya kudin fansa domin su saki yaron.”

An tattaro cewa mahaifin yaron ya biya kudin fansa naira miliyan 1 domin a saki dan nasa.

Sai dai, rundunar yan sandan ta ce bata san da cewar an biya kudin fansa kafin sakin yaron ba.

KU KARANTA KUMA: Ilimin ƴaƴa mata: Hankalin Sarakunan Arewa ya tashi kan wasu jihohi 5

A wani labari na daban, Gwamnan jihar Katsina, Bello Masari, a ranar Litinin, 16 ga watan Nuwamba, ya koka kan ayyukan yan bindiga a jiharsa.

Masari, wanda ya yi magana da manema labarai a Kafur ya bayyana cewa mafi akasarin wadannan miyagun su kan je su haddasa tashin hankali a Katsina sannan su koma mabuyarsu a Zamfara, jaridar The Nation ta ruwaito.

Gwamnan ya yi korafin cewa yan bindigan na yin duk abunda za su iya don wargaza kokarinsa na dawo da zaman lafiya, tsaro da oda a Katsina.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng