ASUU: Gwamnatin Tarayya ba ta cika duka alkawuran da mu ka yi da ita ba

ASUU: Gwamnatin Tarayya ba ta cika duka alkawuran da mu ka yi da ita ba

- Kungiyar Malaman Jami’a ta yi magana game da yajin-aikin da ta ke yi

- Shugaban ASUU ya ce gwamnati ba ta cika duka alkawuran da ta yi ba

- Biodun Ogunyemi ya karyata ikirarin da Minista ya yi na shawo kansu

Kungiyar ASUU ta malaman jami’a ta ce sam ba a kai ga matakin karshe na janye dogon yajin-aikin da ake ta faman yi a jami’o’in gwamnati ba.

Jaridar Vanguard ta rahoto kungiyar ta na cin-karo da ministan kwadago, Dr. Chris Ngige, wanda ya fito ya na nuna yajin-aikin ya kusa zuwa karshe.

A cewar Chris Ngige, an biya wa ASUU shida daga cikin bukatu tara da ta gabatar wa gwamnati.

KU KARANTA: Sai inda karfinmu ya kare a kan makarantun Jami’a - ASUU

Da ya ke hira da Vanguard a ranar 15 ga watan Nuwamba, shugaban kungiyar ASUU, Biodun Ogunyemi ya ce gwamnati ba ta cika alkawuranta ba.

Farfesa Biodun Ogunyemi ya ce: “A iyaka saninmu, babu abin da aka yi wa mutanenmu, kuma ba mu son alkawuran bogi.”

Shugaban ASUU na kasa ya ce: “Bari mu dauki batutuwan daya bayan daya.”

“Albashinmu da aka hana na watanni hudu zuwa takwas, su na nan har yau ba a biya ba. Da an biya, da mun ji. Haka maganar alawus din karin aikin koyarwa.”

KU KARANTA: ASUU: Gwamna Zulum da Bello Matawalle su sa baki

ASUU: Gwamnatin Tarayya ba ta cika duka alkawuran da mu ka yi da ita ba
Sanata Chris Ngige Hoto: www.sunnewsonline.com
Asali: UGC

“Ba a kai ga kafa kwamitin ziyara a jami’o’i ba, idan da an yi hakan, da ‘Yan Najeriya sun ji sunayen wadanda aka zaba kamar yadda gwamnati ta sanar.”

“Ba a duba lamarin kutsen da gwamnatocin jihohi su ke yi wa jami’o’i ba. Ba a koma kan batun sake duba yarjejeniyar 2009 ba.” Inji Farfesa Biodun Ogunyemi.

Shugaban kungiyar ya kuma ce ba a fara dabbakar da yarjejeniyar 2019 ba. Bayan haka kungiyar ta zargi gwamnati da bude mata shafin bogi a dandalin Twitter.

Gwamnatin tarayya a ranar Asabar ta ce shirye-shirye na kan hanya domin ganin an yi wani tsari ga malaman makaranta ta yadda za a gyara harkar malanta.

Ana so ya zama sai masu takardun digiri mai kyawu ne za su rike koyar wa a makarantu.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel