Da duminsa: An kashe mataimakin kwamandan Al-Qaeda

Da duminsa: An kashe mataimakin kwamandan Al-Qaeda

- Wani rahoto ya bayyana cewa an kashe mataimakin Kwamandan Al-Qeada bisa umarnin Amurka a Tehran

- Ana zargin Abdullah da tarwatsa ofisoshin jakadancin Amurka a Tanzaniya da Kenya a shekarar 1998

- Hukumar yaki da ta'addanci ta kasar Amurka ta ce baya hannun hukumomin Kasar kuma gwamnati ta sanya tukuici ga duk wanda ya bada bayani kan yadda za a gano shi

Mataimakin babban kwamandan Al-Qeada da aka gurfanar a Amurka a kan tarwatsa musu ofisoshin jakadanci a Tanzaniya da Kenya a shekarar 1998, rahotanni daga jaridar New York Times ta ruwaito ranar Juma'a cewa an kashe shi a sirrance tun cikin watan Agusta.

Abdullah Ahmed Abdullah wanda ke cikin jerin wanda rundunar FBI ke nema ruwa a jallo, an harbe shi kuma ya mutu a Tehran daga wasu jami'an Isra'ila a bisa umarnin Amurka, jami'ai na musamman sun tabbatar wa jaridar times.

DUBA WANNAN: Gobara ta tashi a ofishin hukumar wutar lantarki na garin Jos

Amurka, Iran, Isra'ila, ko Al-Qeada basu dauki alhakin harin da ya faru a ranar 7 ga watan Agusta lokacin tunawa da ranar fashewar bama-baman Afirka, The Punch ta ruwaito.

Babban shugaban Al-Qeada, Abu Muhammad Al-Masri, an kashe shi tare da ýar sa Miriam, tsohuwar matar Osama bin Laden, a rahoton jaridar Times.

Da duminsa: An kashe mataimakin kwamandan Al-Qaeda
Da duminsa: An kashe mataimakin kwamandan Al-Qaeda. Hoto daga @MobilePunch
Asali: Twitter

Gwamnatin Amurka ta sanya ladan dala miliyan 10 ga duk wanda ya bada wani bayani da zai yi sanadiyar kama shi.

DUBA WANNAN: Kansila ya yi wa matar yayansa mugun duka bayan zarginta da maita

Abdullah shine "mafi wayo da kwarewa wajen tsara hare-hare, baya hannun Amurka ko kuma a hannun hukumomin ta", kamar yadda yake a wata takarda ta hukumar yaki da ayyukan ta'addanci Amurka ta fitar a 2008, a cewar jaridar Times.

Tarwatsa ofisoshin jakadancin a Kenya da Tanzaniya a shekarar 1998 ya janyo mutuwar mutane 224 da kuma raunata fiye da mutane 5,000.

An gurfanar da Abdullah a gaban babbar kotun tarayya a Amurka sakamakon laifin.

A wani labari na daban, Sarkin Saudiyya Salman bin Abdulaziz Al Saud ya kira Shuguba Muhammadu Buhari na Najeriya a wayar tarho, a ranar Alhamis kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Saudiyya ya ruwaito.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164