Da duminsa: An kashe mataimakin kwamandan Al-Qaeda

Da duminsa: An kashe mataimakin kwamandan Al-Qaeda

- Wani rahoto ya bayyana cewa an kashe mataimakin Kwamandan Al-Qeada bisa umarnin Amurka a Tehran

- Ana zargin Abdullah da tarwatsa ofisoshin jakadancin Amurka a Tanzaniya da Kenya a shekarar 1998

- Hukumar yaki da ta'addanci ta kasar Amurka ta ce baya hannun hukumomin Kasar kuma gwamnati ta sanya tukuici ga duk wanda ya bada bayani kan yadda za a gano shi

Mataimakin babban kwamandan Al-Qeada da aka gurfanar a Amurka a kan tarwatsa musu ofisoshin jakadanci a Tanzaniya da Kenya a shekarar 1998, rahotanni daga jaridar New York Times ta ruwaito ranar Juma'a cewa an kashe shi a sirrance tun cikin watan Agusta.

Abdullah Ahmed Abdullah wanda ke cikin jerin wanda rundunar FBI ke nema ruwa a jallo, an harbe shi kuma ya mutu a Tehran daga wasu jami'an Isra'ila a bisa umarnin Amurka, jami'ai na musamman sun tabbatar wa jaridar times.

DUBA WANNAN: Gobara ta tashi a ofishin hukumar wutar lantarki na garin Jos

Amurka, Iran, Isra'ila, ko Al-Qeada basu dauki alhakin harin da ya faru a ranar 7 ga watan Agusta lokacin tunawa da ranar fashewar bama-baman Afirka, The Punch ta ruwaito.

Babban shugaban Al-Qeada, Abu Muhammad Al-Masri, an kashe shi tare da ýar sa Miriam, tsohuwar matar Osama bin Laden, a rahoton jaridar Times.

Da duminsa: An kashe mataimakin kwamandan Al-Qaeda
Da duminsa: An kashe mataimakin kwamandan Al-Qaeda. Hoto daga @MobilePunch
Asali: Twitter

Gwamnatin Amurka ta sanya ladan dala miliyan 10 ga duk wanda ya bada wani bayani da zai yi sanadiyar kama shi.

DUBA WANNAN: Kansila ya yi wa matar yayansa mugun duka bayan zarginta da maita

Abdullah shine "mafi wayo da kwarewa wajen tsara hare-hare, baya hannun Amurka ko kuma a hannun hukumomin ta", kamar yadda yake a wata takarda ta hukumar yaki da ayyukan ta'addanci Amurka ta fitar a 2008, a cewar jaridar Times.

Tarwatsa ofisoshin jakadancin a Kenya da Tanzaniya a shekarar 1998 ya janyo mutuwar mutane 224 da kuma raunata fiye da mutane 5,000.

An gurfanar da Abdullah a gaban babbar kotun tarayya a Amurka sakamakon laifin.

A wani labari na daban, Sarkin Saudiyya Salman bin Abdulaziz Al Saud ya kira Shuguba Muhammadu Buhari na Najeriya a wayar tarho, a ranar Alhamis kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Saudiyya ya ruwaito.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel