Tsaka mai wuya: Kotu ta gurfanar da dan majalisar APC daga arewa saboda rantsuwa a kan karya

Tsaka mai wuya: Kotu ta gurfanar da dan majalisar APC daga arewa saboda rantsuwa a kan karya

- Kotun majistare da ke yankin Wuse, Zone 6, ta gurfanar da mamba majalisar wakilai daga mazabar Billiri/Balanga a jihar Gombe, Mista Victor Mela

- Rundunar 'yan sanda a birnin tarayya ta rubuta korafin zargin Mista Mela da rantsuwa a kan karya yayin da ya cike fom din INEC

- Lauyan da ke kare dan majalisar ya bukaci kotu ta yi sassauci a hukuncin da za ta zartar a kan Mista Mela

Wata kotun majistare da ke zamanta a Wuse, Zone 6, ta gurfanar da mamba a majalisar wakilai, Mista Victor Mela, bisa zarginsa da bayar da bayanan karya ga hukumar zabe ta kasa (INEC) tare da yin rantsuwa a kan cewa gaskiya ne.

Kotun ta ce dan majalisa Mela, mai wakilatar mazabar Billiri/Balanga a majalisar tarayya, ya bawa INEC bayanan karya domin samun damar tsayawa takara a zaben shekarar 2019.

Hukumar 'yan sandan birnin tarayya (FCT), Abuja, ce ta gurfanar da Mista Mela bayan zarginsa da rattaba hannu, a matsayin rantsuwa, a kan bayanana karya da ya bayar yayin cike fom din hukumar INEC mai lamba CF001 gabanin zaben 2019.

DUBA WANNAN: Ba haka bane Farfesa; Shehu Sani ya ci gyaran Zulum a kan sababin fara yakin Boko Haram

Alkalin kotun da ya saurari karar ya saka ranar yanke hukunci a kan karar bayan lauyan da ke kare Mista Mela ya nemi kotu ta yi sassauci a hukuncin da za ta zartar a kan wanda ya ke karewa.

Tsaka mai wuya: Kotu ta gurfanar da dan majalisar APC daga arewa saboda rantsuwa a kan karya
Victor Mela
Asali: Twitter

Hukumar INEC ta bayyana Mista Mela a matsayin wanda ya samu nasarar lashe zaben kujerar zaben dan majalisar wakilai na mazabar Billiri/Balanga a zaben da aka gudanar a cikin watan Fabarairu na shekarar 2019.

DUBA WANNAN: Gwamnatin tarayya ta ware Dangote daga dokar rufe iyakokin kasa

Duk da Ali Isa, dan takarar jam'iyyar PDP, ya kalubalanci nasarar da Mista Mela ya samu a zaben, kotun turabunal da ta daukaka kara da ke Jos sun jaddada nasarar da dan takarar na APC ya samu.

A wani labarin daban da Legit.ng ta wallafa, an sake tsintar gawar matasan 'yammata biyu da mutanen da ba'a san ko su waye ba suka jefar a unguwar Kurmin Mashi da ke cikin garin Kaduna.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng