Jerin sunayen ƴan Nigeria guda 3 da suka lashe zaɓen kujerar majalisar tarayya a Amurka

Jerin sunayen ƴan Nigeria guda 3 da suka lashe zaɓen kujerar majalisar tarayya a Amurka

- Akalla yan Najeriya uku ne suka yi nasara a zaben 2020 na kasar Amurka

- An gudanar da zaben ne a ranar Talata, 3 ga watan Nuwamba

- Esther Agbaje, Oye Owolewa da kuma Nnamdi Chukwuocha ne yan Najeriyan da suka yi nasara a zaben

Ga jerin yan Najeriya uku da suka yi nasara a kasa, kamar yadda rahoton Premium Times ya nuna.

KU KARANTA KUMA: Karshen alewa kasa: An kama makasan dan majalisar jihar Bauchi

Jerin sunayen ƴan Nigeria guda 3 da suka lashe zaɓen kujerar majalisar tarayya a Amurka
Jerin sunayen ƴan Nigeria guda 3 da suka lashe zaɓen kujerar majalisar tarayya a Amurka Hoto: BBC, Sahara Reporters and Nairametrics
Asali: UGC

1. Esther Agbaje

Ms Agbaje ta yi takara domin wakiltan gudunmar 59B a majalisar wakilai ta Minnesota a karkashin jam’iyyar Democrat. Ta lashe zaben da kuri’u 17,396.

Matashiyar mai shekaru 35 wacce ta karanci fannin shari’a a Harvard ta kayar da yar takarar jam’iyyar Republican, Alan Shilepsky da kuma ta jam’iyyar Green Party, Lisa Neal-Delgado a zaben.

Ta wallafa batun nasarar tata a ranar Laraba, 4 ga watan Nuwamba a shafin Twitter.

2. Oye Owolewa

Haifaffen dan Najeriya a karkashin jam’iyyar Democrat, Oye Owolewa, ya lashe zaben kujerar dan majalisa mai wakiltan gundumar Columbia a kasar Amurka.

Bisa ga sakamakon zaben, Oye sami kaso 82.65 cikin 100 wanda ya kai kuri’u 135,234 inda ya kayar da abokan karawarsa Joyce Robinson-Paul wanda ya sami kuri’u 15,541, da kuma Sohaer Syed wanda ya samu kuri’u 12,846.

Oye Owolewa mai shekaru 30, ya fito ne daga yankin Omu-Aran da ke jihar Kwara.

Ya kammala karatun digirin digir-gir dinsa a fannin Kimiyyar Harhada Magunguna daga Jami’ar Norteastern da ke birnin Boston a kasar ta Amurka.

KU KARANTA KUMA: Dan Najeriya ya lashe zaben kujerar majalisar wakilai a Amurka

3. Nnamdi Chukwuocha

Nnamdi Chukwuocha ya sake lashe zabe a matsayin dan majalisar wakilai na Delaware daga gudunma ta 1.

A matsayinsa na dan jam’iyyar Democrat da bai da abokin hamayya, ya lashe kaso 100 na kuri’un wanda yayi daidai da kuri’u 7,640.

An zabi Chukwuocha domin ya wakilci gudunma ta 1 a majalisar wakilai ta Delaware a 2018.

Yana da digiri a kan ilimin tarihi da digiri na biyu kan aikin jama’a daga jami’ar jihar Delaware, yana da tarin sani kan siyasar cikin gida a jihar.

A gefe guda, 'Yar majalisar wakilai a Amurka, Ilhan Omar, ta sake lashe zabenta a matsayin mai wakiltan mazabar Minnesota ta 5, Minneapolis, a jihar Minnesota.

Ihlan, 'yar shekara 38 ta doke abokin hamayyarta na jam'iyyar Republican Lacy Johnson, wanda bakin fata ne kuma attajiri, da kashi 64.6% - 25.9% na kuri'u, Aljazeera ta ruwaito daga The Associated Press.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng