Kasar Masar za ta mayar da yan Najeriya 7 gida saboda zanga-zangar EndSARS

Kasar Masar za ta mayar da yan Najeriya 7 gida saboda zanga-zangar EndSARS

- Hukumomi a Masar sun ce za su dawo da wasu 'yan Najeriya gida, sakamakon gudanar da zanga-zangar EndSARS ba tare da neman izini ba

- Shugabar hukumar kula da yan Najeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa ce ta tabbatar da hakan

- Mutanen dai sun shiga sahun masu gudanar da zanga-zangar kawo karshen cin zarafin da yan sanda ke yi wa alúmma a ranar 18 ga watan Oktoba

Shugabar hukumar kula da yan Najeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa, a jiya Litinin, 2 ga watan Nuwamba, ta bayyana cewa za a dawo da bakwai daga cikin yan Najeriya takwas da suka gudanar da zanga-zangar EndSARS a Masar.

A wasu jerin wallafa da tayi a shafin Twitter, Dabiri-Erewa ta ce bayan kamunsu, sun roki hukumar da ta sanya baki sannan ta tabbatar da sakinsu.

Kasar Masar za ta mayar da yan Najeriya 7 gida saboda zanga-zangar EndSARS
Kasar Masar za ta mayar da yan Najeriya 7 gida saboda zanga-zangar EndSARS Hoto: @daily_trust
Asali: Twitter

“Karin bayani kan yan Najeriya takwas da aka tsare a birnin Cairo saboda yin zanga-zanga ba tare da izini ba: mahukunta a kasar Masar sun ce za a dawo da bakwai daga cikin yan Najeriya takwas da suka gudanar da zanga-zanga a ranar 18 ga watan Oktoba gida Najeriya saboda rashin takardar izinin zama/biza.

“Dan Najeriya daya daga cikinsu wanda keda takardar zama zai kammala tantancewarsa daga ministan cikin gida na Rasa, Mahmoud Tawfik, bayan ya dauki rantsuwar kin sake aikata wani abu ba tare da izinin mahukunta ba yayin kasancewarsa a kasar,” in ji ta.

Idan za a tuna an kama yan Naeriya takwas a Cairo, Masar, kan yin zanga-zanga a kan cin zarafin yan sanda da kashe-kashe a Najeriya.

KU KARANTA KUMA: Kannywood: Babban darakta Falalu dorayi ya yi wa Rahama Sadau shagube a kan shigar da ta yi

KU KARANTA KUMA: Ibrahim Sharukan ya yi zazzafan martani a kan hoton Rahama Sadau, bidiyo

A gefe guda, hukumar yan sandan Najeriya ta bayyana cewa ba za ta tursasa ma kowani jami’in dan sanda komawa bakin aiki ba, jaridar Premium Times ta ruwaito.

Hukumar PSC din ta bayyana hakan ne a ranar Lahadi, 1 ga watan Nuwamba, a cikin wata sanarwa daga Shugaban harkokin labaranta da hulda da jama’a, Ikechukwu Ani.

Jawabin martani ne ga wata wallafar jarida wacca ta bayyana cewa hukumar ta yi barazanar korar duk jami’an da suka ki dawowa bakin aiki.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng