Kungiyar Oba ta ji haushin amfani da karfin bindiga ga ‘Yan zanga-zanga

Kungiyar Oba ta ji haushin amfani da karfin bindiga ga ‘Yan zanga-zanga

- Kungiyar Sarakunan Yarbawa sun soki harbe masu zanga-zanga a Lekki

- Sarakai a Kwara, Kogi, Osun, Oyo, Ondo, Ekiti, Legos, Ogun sun yi jawabi

- Sun ce bai kamata a harbe Bayin Allah da ba su dauke da kayan fada ba

Kungiyar Yoruba Obas Forum ta Sarakunan kasar Yarbawa ba su ji dadin abin da ya faru na harbe wasu matasa da su ka fita zanga-zanga ba.

Wannan kungiya ta manyan kasar su na koka wa da abin da su ka kira amfani da karfin bindiga a kan matasan da ba su dauke da makamai.

Jaridar Vanguard ta rahoto cewa wannan kungiya ta kunshi Sarakunan gargajiyan da su ka fito daga duka jihohin da ke da Yarbawa a Najeriya.

KU KARANTA: #EndSARS: Ya kamata Shugaban kasa ya yi amfani da hikima – Sultan

Wadannan jihohi kuwa su ne: Osun, Oyo, Ondo, Ekiti, Legos, Ogun, sai kuma Kwara da Kogi.

A wata takarda da sarakan su ka fitar ga ‘yan jarida, sun nuna rashin jin dadinsu game da abin da ake zargin sojoji sun yi a ranar Talata a Lekki, Legas.

Su ka ce: “Ya na da muhimmanci a tuna ba a raba mulkin farar hula da damar mutane na fitowa su yi zanga-zangar lumana domin ba gwamnati shawara.”

“Hakkin yin zanga-zangar lumana ya na cikin damar da aka bada a karkashin kundin tsarin mulkin Najeriya da kundin kare hakkin mutanen Afrika.”

KU KARANTA: INEC ta fasa zabe a Legas da Bayelsa, dsr saboda zanga-zanga

Kungiyar Oba ta ji haushin amfani da karfin bindiga ga ‘Yan zanga-zanga
Sarakunan Kudu Hoto: Pulse.ng
Asali: UGC

Kungiyar ta kuma ce: “Abin mamaki ne da da-na-sani da takaici a ga wasu sojoji da ba a sansu ba, su na harbin mutanen da su ke kiran gwamnati ta gyara.”

Sarakan a matsayinsu na iyayen kasa, sun bada shawarar a hakura da ramuwa, a zauna ayi sulhu.

Gwamna Dave Umahi hankali ya ce lamarin #EndSARS ya koyawa shugabanni hankali, ya kuma ba matasa hakuri a madadin sauran masu mulki a kasar.

Bayan haka, Umahi ya ba shugabannin shawara su fara jawo matasan Najeriya a jikinsu.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel