Da duminsa: Najeriya ta tabbata cibiyar mutuwar yara masu kasa da shekaru 5 a duniya

Da duminsa: Najeriya ta tabbata cibiyar mutuwar yara masu kasa da shekaru 5 a duniya

Najeriya ta sha gaban kasar India a matsayin babbar cibiyar mutuwar kananan yara masu kasa da shekaru biyar, kamar yadda majalisar kula da kananan yara ta duniya ta bayyana a 2020.

Wannan cigaban ya faru kasa da shekaru biyu da bankin duniya ta yi hasashen aukuwarsa.

A 2018, bankin duniya ta ce Najerya zata sha gaban kasar India a yawan mace-macen kananan yara masu kasa da shekaru biyar amma sai 2021.

Kamar yadda bankin duniyan ya bayyana, kasar India ta samu kiyasin mutuwar a kalla kananan yara 989,000 a 2017, yayin da Najeriya ke da 714,000 a wannan shekarar.

Kamar yadda rahoton UNICEF ya bayyana, ya ce Najeriya ta samu mutuwar yara masu kasa da shekaru biyar 858,000 a 2019, yayin da India ta samu 824,000 a 2019, inda ta kasance a mataki na biyu a duniya.

Rahoton wanda ya duba shekaru goma-goma, ya bayyana cewa kashi 49 na mutuwar kananan yara masu kasa da shekaru 5 a duniya yana faruwa ne a kasashe biyar a duniya. Sune: Najeriya, India, Pakistan, Kongo da Ethiopia.

"Najeriya da India kadai suna da kashi daya bisa uku na dukkan mace-macen kananan yara a duniya," rahoton yace.

Da duminsa: Najeriya ta tabbata cibiyar mutuwar yara masu kasa da shekaru 5 a duniya
Da duminsa: Najeriya ta tabbata cibiyar mutuwar yara masu kasa da shekaru 5 a duniya. Hoto daga reviewsgeek
Source: Getty Images

KU KARANTA: Za'a yiwa daliban jihar Ogun karin aji kai tsaye ba tare da sun zana jarrabawa ba idan suka koma makaranta a ranar 21 ga watan Satumba - Dapo Abiodun

Rahoton ya kara da cewa, mace-macen yara masu shekaru kasa da biyar ya ragu da a kalla kashi 60 tun daga 1990.

Amma kuma, majalisar dinkin duniya ta bayyana damuwarta a kan yuwuwar dawowar mace-macen kananan yaran a 2020. Hakan babban kalubale ne ga nasarar da aka samu a baya.

"A yayin da har yanzu ba a san illar da kuma yawan mutuwar kananan yara da matasa da cutar korona ta janyo ba, yuwuwar cigaba da mace-macen kananan yara a 2020 abun tsoro ne," yace.

“Yawan mutuwar kananan yaran ta ragu da kusan kashi 60 tun daga 1990 zuwa 2019. Amma kuma akwai babban kalubale a wannan shekarar.

“Duk da wannan cigaban, yara miliyan 5.2 na rasuwa kafin su cika shekaru biyar a 2019 kadai. Abun takaicin shine yadda yaran ke mutuwa sakamakon cutukan da za a iya magancewa."

A wani labari na daban, hukumar kashe Gobara ta Jihar Kano ta ce wani yaro dan shekara bakwai, Umar Ado ya mutu a cikin rijiya a Unguwa Uku by Yarabawa Street a karamar hukumar Tarauni na jihar.

Sanarwar ta fito ne daga bakin mai magana da yawun hukumar, Alhaji Saidu Mohammed a ranar Laraban wannan makon kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Mohammed ya ce lamarin ya faru ne a ranar Talata da yamma a lokacin da marigayin ya tafi rijiyar domin ya diba ruwa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng