Bankuna 7 da Buhari zai ciwo bashin $22.7bn da majalisa ta bashi dama

Bankuna 7 da Buhari zai ciwo bashin $22.7bn da majalisa ta bashi dama

Bayan ganawar sirri sakamakon sabanin da aka fara samu a zauren majalisa, Majalisar dattawan tarayya ta baiwa shugaba Muhammadu Buhari daman karbo bashin $23bn (dala bilyan 22,798,446,773).

Shugaba majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis bayan gajeren mujadalan da akayi kan hakan.

Yayinda ake muhawara kan lamarin, shugaban marasa rinjaye, Eyinnaya Abaribe, ya gargadi majalisar kan baiwa shugaban kasa daman karbo bashin duka kudaden a lokaci guda.

Ya bada shawaran cewa a yi muhawara kan ayyukan da zaa karbo bashi kansu daya bayan daya. Amma shugaban majalisar datawa ya bayyana rashin amincewarsa da hakan.

Bayan haka sai aka fara tafka muhawara kan lamarin har aka fara samun sabani kuma haka ya tilasta yan majalisar saka labule.

Za ku tuna cewa a 2019, shugaba Muhammadu Buhari ya bukaci karbo rancen kudi daga kasar waje lokacin Bukola Saraki amma suka hanashi.

A yanzu haka, ana bin Najeriya bashin N26.215 trillion.

Kimanin kashi 70 cikin 100 na bashin zai zo ne daga bankin kasar Sin yayinda za a karbo sauran daga bankin duniya da sauransu.

Ga jerin wurare 7 da Buhari zai karbo bashi da adadin da za a karbo wurinsu

1. Bankin shiga da fice na kasar Sin ($17bn)

2. Bankin Duniya ($2.95bn)

3. Bankin cigaban Afrika ($1.88bn)

4. Bankin cigaban Musulunci ($110m)

5. Hukumar hadin kai da kasashen waje na kasar Japan ($200m).

7. Bankin cigaban kasar Jamus ($20m)

8. Hukumar cigaban kasar Faransa ($480m)

Bankuna 7 da Buhari zai ciwo bashin $22.7bn da majalisa ta bashi dama
Bankuna 7 da Buhari zai ciwo bashin $22.7bn da majalisa ta bashi dama
Asali: UGC

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel