Masu garkuwa da mutane sun saki basaraken da suka sace a Kano

Masu garkuwa da mutane sun saki basaraken da suka sace a Kano

A ranar Alhamis ne dagacin garin Karshi dake karkashin karamar hukumar Rogo ya shaki iskar 'yanci bayan wasu 'yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun yi awon gaba da shi tun ranar Litinin.

An sace dagacin ne ranar Litini a garinsa na Karshi mai makwabtaka da jihar Kaduna ta kudancin jihar Kano.

Masarautar Karaye da rundunar 'yan sandan jihar Kano sun tabbatar da sace basarake a cikin sanarwa daban - daban da suka fitar.

Bayan sace Basaraken ne rundunar 'yan sanda a jihar Kano ta sanar da cewa ta tura wata tawagar jami'anta na musamman domin kubutar da dagacin da kuma kama 'yan bindigar da suka yi awon gaba da shi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng