Sakamakon Zabe: Ganduje ya yi nasara a kananan hukumomi 3 na jihar Kano

Sakamakon Zabe: Ganduje ya yi nasara a kananan hukumomi 3 na jihar Kano

A yayin da hukumar zabe da kasa mai zaman kanta ta fara bayyana sakamakon zaben gwamnoni da 'yan majalisun dokoki da aka gudanar a jiya Asabar, 9 ga watan Maris, mun samu cewa, gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi nasara cikin wasu kananan hukumomi uku na jihar.

Cikin sakamakon kananan hukumomi hudu da hukumar INEC ta wassafa sakamakon su a yau Lahadi, mun samu cewa, gwamna Abdullahi Ganduje ya yi nasara cikin uku daga cikin su kamar yadda majiyar jaridar Legit.ng ta ruwaito.

Sakamakon Zabe: Ganduje ya yi nasara a kananan hukumomi 3 na jihar Kano
Sakamakon Zabe: Ganduje ya yi nasara a kananan hukumomi 3 na jihar Kano
Asali: Depositphotos

Kananan hukumomin hudu na jihar Kano da hukumar INEC ta bayyana sakamakon su kamar yadda shafin jaridar The Punch ya ruwaito sun hadar da; Albasu, Bebeji, Karaye da kuma karamar hukumar Bunkure.

KARANTA KUMA: Sakamakon Zabe: Hukumar 'yan sanda ta gargadi al'umma kan gudanar da bikin murna a jihar Kano

Turawan zaben na kananan hukumomin Albasu, Farfesa Mustapha Hassan Bichi, karamar hukumar Bunkure, Farfesa Nuruddeen Magaji da kuma na karamar hukumar Karaye, Farfesa Bello Idris Tijjani, sun tabbatar da nasarar dan takarar kujerar gwamnan jihar Kano na jam'iyyar APC da ya kasance Gwamna Ganduje.

Sai dai Gwamna Ganduje cikin karamar hukumar Bebeji, ya sha kasa a hannun abokin adawar sa na jam'iyyar PDP, Abba Kabir Yusuf kamar yadda Baturen zabe Farfesa Ibrahim Barde ya bayyana.

Ga yadda sakamakon zaben ya kaya cikin kananan hukumomin hudu tsakanin Ganduje da Abba kamar yadda hukumar INEC ta zayyana.

Karamar Hukumar Albasu

APC: 25,358

PDP: 18,401

Karamar Hukumar Bunkure

APC: 20,271

PDP: 19,932

Karamar Hukumar Karaye

APC: 18,770

PDP: 17,163

Karamar Hukumar Bebeji

PDP: 18,533

APC: 17,418

Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da Shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo cikin shafukan mu na zaurukan sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel