An ja daga a birnin Shehu yayinda APC ke kokarin tsige Tambuwal

An ja daga a birnin Shehu yayinda APC ke kokarin tsige Tambuwal

-Jam’iyyar APC na kokarin ganin ta tuge Gwamna Tambuwal daga kujerar gwamnan jihar Sokoto

- Dan takarar jam’iyyar, Ahmed Aliyu Sokoto, ya bukaci mutanen jihar da su zabe shi da shugaban kasa Muhammadu Buhari kan rashin ayyukan ci gaba a jihar

- Sanata Aliyu Wamakko, yace dukkanin yan takara na APC a zabe mai zuwa masu martaba ne, inda ya bukaci mutane da su yi waje da jam’iyyar PDP a jihar saboda rashin kokarinta

Rahotanni sun kawo cewa gabannin zaben gwamna na 2019, kullin da ake yi don tsige gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal ya girmama.

A wajen kamfen din dan takarar gwamna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Dange/Shuni a ranar Lahadin da ya gabata, dan takarar jam’iyyar, Ahmed Aliyu Sokoto, ya bukaci mutanen jihar da su zabe shi da shugaban kasa Muhammadu Buhari kan rashin ayyukan ci gaba a jihar.

An ja daga a birnin Shehu yayinda APC ke kokarin tsige Tambuwal
An ja daga a birnin Shehu yayinda APC ke kokarin tsige Tambuwal
Asali: Facebook

A nashi bangaren, shugaban jam’iyyar a jihar, Sanata Aliyu Wamakko, yace dukkanin yan takara na APC a zabe mai zuwa masu martaba ne, inda ya bukaci mutane da su yi waje da jam’iyyar People Democratic Party (PDP) a jihar saboda rashin kokarinta.

KU KARANTA KUMA: Matakin farko da ya kamata gwamnati ta dauka na yaki da cin hanci da rashawa shine tabbatar da yiwa talakawa aiki - Atiku

A wani lamari makamancin haka APC a jihar tace mambobin PDP 10,900 sun sauya sheka zuwa APC a kananan hukumomin Tambuwal da Dange /Shuni da ke jihar.

Hakan na kunshe ne a wani jawabi dauke da sa hannun mataimakinsa a kafofin watsa labarai, Bashir Rabe Mani, a karshen makon da ya gabata.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng