Garabasa: Wani mai adai-daita sahu a Kano yana daukar mutane kyauta albarkacin watan Ramadana

Garabasa: Wani mai adai-daita sahu a Kano yana daukar mutane kyauta albarkacin watan Ramadana

A wani yunkuri na neman rahamar ubangijin sa, wani matashi mai sana'ar adaidaita Sahu ko Keke Napep a garin Kano ya shelanta garabasar daukar mutane kyauta albarkacin shigowar watan azumin Ramadana.

Garabasa: Wani mai adai-daita sahu a Kano yana daukar mutane kyauta albarkacin watan Ramadana
Garabasa: Wani mai adai-daita sahu a Kano yana daukar mutane kyauta albarkacin watan Ramadana

KU KARANTA: Sojojin saman Najeriya sun yi luguden wuta ga 'yan Boko Haram

Matashin mai suna Umar Saidu dai an ganshi ne da takardar makale a bayan adai-daita sashun nashi dauke da rubutun da ke nuni da bayanin da muka bayar a sama a cikin harshen turanci.

Legit.ng ta samu cewa hoton sa din dai ya dauki hankalin jama'a sosai a shafukan sadarwar zamani dukkan fadin kasar nan musamman ma a tsakanin musulmai wadanda suka gode masa tare da sa masa albarkar.

Mai karatu dai zai iya tuna cewa an fara azumin watan Ramadana a kasashe da dama a fadin duniya ne a ranar Alhamis din da tagata ciki kuwa hadda kasar Najeriya.

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel