An Samu Rudani kan Rasuwar Dan Wasan Najeriya a Kasar Waje

An Samu Rudani kan Rasuwar Dan Wasan Najeriya a Kasar Waje

  • Rundunar ‘yan sandan Uganda na bincike kan mutuwar dan kwallon Najeriya, Abubakar Lawal, wanda aka ce ya fado daga bene na uku
  • Lawal yana ziyarar wata budurwa ‘yar Tanzaniya a dakin da take zama a katafaren kasuwa a Kampala, daga baya aka same shi a kasa
  • Kungiyoyin Vipers SC da Kano Pillars sun nuna alhinin mutuwarsa, yayin da ake kira ga gwamnati ta Najeriya ta binciki abin da ya faru da shi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kampala, Uganda - Rundunar ‘yan sandan Uganda ta fara bincike kan mutuwar dan wasan Najeriya, Abubakar Lawal.

Rahotanni sun tabbatar da marigayin ya fado daga bene na uku a wata kasuwa da ke birnin Kampala a kasar Uganda.

Tsohon dan wasan Najeriya da Kano Pillars ya rasu
Yan sanda a Uganda suna binciken mutuwar tsohon dan wasan Najeriya da Kano Pillars. Hoto: Uganda Police Force.
Asali: Facebook

Menene dalilin mutuwar dan wasa Najeriyan?

Dan wasan mai shekara 29, wanda tsohon dan kwallon Najeriya U-20 ne, yana taka leda a kungiyar Vipers SC kamar yadda shafin Facebook na Uganda Police Force ya wallafa.

Kara karanta wannan

An bankado umarnin Tinubu da zai illata Arewa, NARTO ta gargadi gwamnati

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahotanni sun nuna cewa ya kai ziyara ne wurin wata budurwa ‘yar Tanzaniya a dakin da take zama a kasuwar Voicemall.

Majiyoyi sun bayyana cewa jami’an tsaro na duba bidiyon CCTV da kuma bincike don gano abin da ya faru kafin faduwarsa.

Budurwar marigayin ta yi magana kan lamarin

Budurwarsa, Omary Naima, ta shaida wa ‘yan sanda cewa ta bar shi a dakin yana hada shayi, amma daga baya an same shi a kasa da misalin 8:00 na safe.

Rahoton ‘yan sanda ya bayyana cewa tsohon dan wasan Najeriya ya iso kasuwar da motarsa mai lamba UBQ 695G don ganin budurwarsa Omary Naima, wacce take dakin 416.

Naima ta ce ta bar Lawal a daki, amma daga baya ta ji cewa ya fado daga baranda, lamarin da ke kara jawo tambayoyi.

An gaggauta kai shi asibitin Entebbe Referral, a nan likitoci suka tabbatar da mutuwarsa nan take.

Kara karanta wannan

Dubu ta cika: Ƴan sanda sun cafke hatsabibin barawon da ya addabi Jigawa da sata

Kungiyar Vipers SC ta fitar da sanarwa, tana nuna alhinin rasuwar Lawal, tare da mika ta’aziyya ga iyalansa da magoya bayansa.

Kungiyar Kano Pillars ta yi jimamin rasuwar tsohon dan wasanta

Kano Pillars ta tura sakon ta'azziya

Kano Pillars, tsohuwar kungiyarsa a Najeriya, ita ma ta fitar da sanarwa, suna cewa mutuwarsa babban rashi ne ga masoya kwallon kafa, cewar Premium Times.

A baya an ce ya mutu ne a hatsarin babur a Entebbe Road, amma binciken ‘yan sanda ya nuna ya fado daga bene na kasuwa.

Saboda rashin fayyace gaskiya, ana kiran gwamnatin Najeriya da ta shiga tsakani don tabbatar da an gudanar da bincike mai zurfi.

Lawal ya koma Vipers SC a watan Yuli 2022 bayan ya shafe shekaru biyu yana taka leda a AS Kigali ta Ruwanda.

Yan kwallon Kano Pillars sun yi hatsari

Kun ji cewa rahotanni sun nuna cewa 'yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars sun yi hatsari a kan hanyarsu ta zuwa filin wasan Jos.

Kara karanta wannan

Yadda adawar manyan yan siyasar Najeriya za ta shafi tasirin gwamnatin Tinubu

An ce tawagar Kano Pillars ta 'yan kasa da shekaru 19 ta yi hatsarin motar ne ranar Talata, 22 ga watan Oktobar 2024.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.