An Fatattaki Kocin Manchester United bayan Ajiye Munanan Tarihi

An Fatattaki Kocin Manchester United bayan Ajiye Munanan Tarihi

  • Rahotanni na nuni da cewa kungiyar kwallon kafar Manchester United ta kori kocinta, Erik Ten Hag bayan shan kaye da suka yi
  • Ana hasashen cewa an kori kocin ne bisa yadda kungiyar kwallon kafar Manchester United ta gaza tabuka abin kirki a bana
  • Ko a wasan karshe da Manchester United ta buga da West Ham a ranar Lahadi da ta wuce, kungiyar ta sha wani kaye mai ban ciwo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

London - Rahotanni da suka fito na nuni da cewa kungiyar kwallon kafar Manchester United ta kori kocinta, Erik Ten Hag a yau Litinin.

A shekarar 2022 ne Erik Ten Hag ya fara aiki da Manchester United kuma a karon farko kusan ya tabuka abin kirki.

Kara karanta wannan

Wulakanta 'yan wasan Super Eagles ya jefa kasar Libiya a matsala, CAF ta yi hukunci

Erik Ten
An kori kocin Manchester United
Asali: Facebook

Rahoton BBC ya nuna cewa Manchester United ta fara shirin nada mukaddashin koci da zai rike kungiyar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An kori kocin Manchester United, Ten Hag

Mirror ta ruwaito cewa kungiyar kwallon kafar Manchester United ta kori kocinta, Erik Ten Hag a yau Litinin, 28 ga watan Oktoba.

Erik Ten Hag ne kocin Manchester United na biyar tun bayan ritayar Sir Alex Ferguson a shekarar 2013.

Dalilin korar kocin Manchester United

Ana hasashen cewa rashin tabuka abin kirki a kakar bana na cikin dalilan korar Erik Ten Hag daga Manchester.

Kungiyar Manchester United ta dawo ta 14 a teburin gasar Premier bayan shan kaye a ranar Lahadi da ta wuce.

Kokarin da Erik ya yi a Manchester Utd

A kakar wasan da ta wuce kungiyar Manchester United ta lashe kofin FA a karkashin jagorancin Erik Ten Hag.

Kara karanta wannan

Ana matsalar lantarki. 'yan Arewa sun dura kan Tinubu, sun ragargaje shi

Haka zalika a shekarar 2022 da Erik ya zo Manchester ya jagoranci kungiyar zuwa na uku a gasar Premier.

A yanzu haka dai kungiyar ta sanar da cewa Van Nistelrooy zai cigaba da jagorancin kungiyar kafin a samu koci na dindindin.

CAF ta hukunta Libya kan Najeriya

A wani rahoton, kun ji cewa wulakanta 'yan wasan Super Eagles ya jefa kasar Libiya a cikin matsala yayin da CAF ta sanar da yanke hukunci.

Hukumar CAF ta ce ta kama Libiya da karya dokokin dokokin gasar cin kofin Afrika da kuma na CAF a abin da ta yi wa tawagar Najeriya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng